Saturday, July 18, 2015

SALLAR BANA : TSAKANIN MUSULMI DA ' YAN SHIAH


SALLAR BANA: TSAKANIN MUSULMI DA 'YAN SHIAH A NAJERIYA!!!

Abin farin ciki ne ainun a wad'annan lakuta ganin yadda kan al'ummar Musulmi a Najeriya ya had'u dangane da batun d'auka da kuma aje Azumi. Hakan babbar nasara ce, kuma alamu ne da suke nuna cin Nasara, domin, a baya mun shaida yadda aka dinga samun sab'ani wajen ganin watan Ramadan da kuma na Shawwal. Inda hukumomi zasu bayar da sanarwa amma wasu su k'ek'asa su ce basu yadda ba, sai sun gani da idonsa,  dan kawai haifar da sab'ani tsakanin Musulmi.

Cikin hukuntawarsa Subhanahu Wata'ala masu wancan ra'ayi sun fara dawowa daga rakiyarsa, inda wannan lokuta ake kara tsuke bakin sab'anin baki daya. Musulmi a kusan gaba d'ayan Najeriya sun d'auki Azumi tare sun kuma yi Sallah tare. Ko Shakka babu wannan zai baiwa Musulmin Najeriya karfi na tunkarar manyan abokan gaba wato SHIAH.

Da yake su mabiya addinin Shiah kullum burinsu shi ne a samu sab'ani tsakanin al'ummar Musulmi,  da burin Kada kai ya had'u. Hakan ta sanya suke kokarin ganin sun tabbatar da sab'anin sun d'auki Azumi daban sun kuma yi Sallarsu daban, sab'anin Musulmi da suka bi Umarnin mai alfarma Sarkin Musulmi Sultan Saad wajen dauka da kuma aje Azumi.  

A har kullum abinda ya kamata mutane su gane kuma su fahimta shi ne cewar, babu wad'an da suke kokarin kawo rarrabuwa ko wargaza zaman lafiya tsakanin al'ummar Musulmi kamar 'yan Shiah. Shugabansu kuma jagoransu Ibrahim El Zakzany shi ne kullum yake ihu da karad'in cewa "HADIN KAI"  amma gashi zahirin sa ya nuna tacacce mayaudari  ne, kullum yaudarar mabiyansa yake da sunan had'in kai, amma kuma ga shi a zahiri yana k'ok'arin tabbatar da samun b'araka da rarrabuwa. 

Daman kuma mun kwana da sanin kokarin cusa rarrabuwa tsakanin Musulmi shi ne abinda 'yan Shia suke ta fatan ganin dorewarsa a kowacce irin al'umma. In sha Allah kuma ba zasu Ci Nasara ba, kamar yadda aka samu wannan had'in kai na al'ummar Musulmin Najeriya, haka za'a  cigaba da samu. Allah ka kara tabbatar da had'in kai tsakanin Musulmi. Ya Allah duk wadan da suke kokarin ganin bayan Musulunci da Musulmi Allah kaga bayansu,  Allah ka bak'anta musu rai da ganin cigaban Musulunci.

Muna addu'ah da sunayan Allah tsarkaka madaukaka Ya Allah ka nesanta mu da zurriyar mu daga Shianci. Allah ka fahimtar da mu addinin Musulunci,  Allah ka bamu lafiya da zaman lafiya. Ya Allah Kada ka baiwa 'yan Shiah nasara a cikin dukkan lamuransu duniya da Lahira. Allah ka taimaki Musulunci da Musulmi.

YASIR RAMADAN GWALE​
18-07-2015

No comments:

Post a Comment