Friday, October 3, 2014

Ta'aziyar Galadiman Kano



GALADIMAN KANO: Alhaji Tijjani Hashim Galadiman Kano kamar yadda 'yan uwa da dama suka sani a yau da safe muka wayi gari da labarin rasuwarsa a babbsn birnin tarayya Abuja wanda ake shirin yin jana'izarsa yanzu. Muna adduar Allah ya jikansa ya gafarta masa, ba shakka rashin Galadima babban rashi ne, domin shi uba ne na al'umma wanda kullum kofarsa a bude take dan taimakawa Talakawa da masu karamin karfi, Galadima ya samu shaida a wajen mutane da yawa wajen taimakawa wadan da aka zalunta ko aka dannewa hakkinsu.

A baya bayan nan Galadima ya taimakawa Addini sosai kuma ya taimaki masu addini sosai. Rashinsa bai tsaya ga Masarautar Kano kadai ba, wannan rashi ne da ya shafi al'umma gaba daya. Allah ya jikansa ya gafarta masa, kurakuransa Allah ya kankare su.

A madadina da Zainab muna mika sakon ta'aziyarmu ga Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sunusi II da Gwamnatin Kano da kuma al'ummar Kano baki daya. Allah ya kyauta namu karshen.

29-09-2014

No comments:

Post a Comment