Wednesday, October 29, 2014

APC: Kwankwaso Yaci Zabe A Bashi Abinsa

Gwamna Rabiu Kwankwaso

APC: KWANKWASO YACI ZABE A BASHI ABINSA

Jiya talata 28 ga oktoban nan muka shaida yadda Miliyoyin 'yan jam'iyyar APC daga ko ina a fadin Najeriya suka hallara a Habuja babban birnin tarayya dan nuna goyan bayansu ga takarar Gwamna Kwankwasiya Amanaa matsayin shugaban kasa wanda zai yiwa jam'iyyar takara. Wadan da suka samu halartar taron sun shaida mana cewar Habuja tayi cikar kwari babu masaka tsinke, duk inda ka duba Jan Kai kawai ake kwalli da shi, mata da maza.

Ance duk wanda yake takara a APC jiya cikinsa ya duri ruwa. Saboda kaddamar da takarar mai girma gwamna a jiya ta yamutsa hazo, kuma ta nuna a fili inda mutane suka karkata. Dan kuwa masu abin (jama'a) sunce sun ji sun gani Kwankwasiyya Nigeria. A sabida haka muke yiwa Shugaban Kasa mai jiran gado murna da fatan alheri. Duk da yake ni ba dan wannan jam'iyyar bane, amma ya zama dole a matsayina na dan Kano nayi murna akan irin yadda Najeriya gaba daya kwata ta hadu tace sai mutumin Kano. Wannan karamci ne akai mana kuma mun gode.

Ina kuma isar da sakon taya murna ga Shugaban kasa mai jiran gado. Ina kuma fatan idan lokacin rantsuwa yayi a aiko min da goran gayyata dan mu hadu a Habuja mu shaida rantsar da Gwamna Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin Shugaban Najeriya na goma sha shida. Kwangwaratuleshan ga abokina Auwalu Lawan Aranposu akan wannan Nasara da suka samu. Ina kuma fatan źa'a dinga kulawa da hakkin makwabtaka da zumuncin da ke tsakaninmu idan an shiga Villa.

Ina kuma amfani da wannan dama wajen yin jaje ga 'yan Bahariyya suKwamared Baban Shareek Gumel da Ibrahim Sanyi-Sanyi da fatan zasu dauki dangana. Shima dan uwana Sunusi Musa ina masa jaje da Atiku Abubakar bai samu wannan nasara ba, shima dan uwa Bashir Ahmad ina tayaka alhini da Sam Nda bai samu wannan nasara ba. Ina kuma fatan zaku hadu dan dafawa mai girma Shugaban kasa mai jiran gado domin ciyar da Najeriya gaba.

29-10-2014

No comments:

Post a Comment