Friday, October 3, 2014

Dakta Habibu Sani Babura



DAKTA HABIBU SANI BABURA (Talban Babura): Ina amfani da wannan dama nayi murna na kuma nuna farin ciki da godiya ga Gwamnatin Jimhuriyyar Nijar karkashin Jagirancin Shugaba Mouhammadou Issoufou bisa ga lambar girma ta kasa da ya baiwa Dakta Habibu Sani Babura.

Ba shakka munyi farin ciki da wannan karramawa da aka yi mana. Wannan ya kara nuna mana irin zumunci da 'Yan uwatanka ta makwabtaka tsakanin Nijar da Najeriya. Muna godiya ga Gwamnati da al'ummar kasar Nijar baki daya.

Dakta kuma muna kara taya shi murna. Muna kuma yi mada addu'ar Allah ya kara masa lafiya da nisan kwana. A madadin ni da Zainab muna taya shi murnar wannan lambar girma da ya samu.

Yasir Ramadan Gwale
01-10-2014

No comments:

Post a Comment