Thursday, April 3, 2014

Wa Ye Zai Kashe Malam Yasir Ramadan Gwale?

WA YE ZAI KASHE MALAM YASIR RAMADAN GWALE

Daga Sheriff Ibrahim Muhammad Almuhajir

Abokina Yasir Ramadan Gwale yayi wani rubutu akan hayaniyar da ta auku a Funtua sai wani ya aiko mishi da sakon zai kasheshi. To bari ka ji in kana son ka sheshi yasir dan Gwale ne a Kano. bismillah in ka yanka ka kawo mana kanshi muna jiranka.

KUMA KUJI

Wani corper yayi rubutu da ya ambaci sunan manzo da mahaifiyar shi Amina da cin zarafi, to yaya zaayi idan aka samu wannan labari,

1- Kasheshi za'ayi kai tsaye.
2- Kona chochi coci za'ayi.
3- Kashe Kirista za'ayi a sace dukiyar su.
4- Ko bincike Malamai da masu mulki ke da hakkin yi alamarin ko gama gari mutane.

Tabbas duk mai hankali dalibin ilmi ingantacce ya san amsar wannan tambaya, Allah taala yace
يا أيها الذين آمنوا إن جائكم فاسق بنبإ فتبينوا أن تصيبوا قوما بجهالة فتصبحوا على ما فعلتم نادمين...واعلموا أن فيكم رسول الله.......
Kowa ya san abunda wannan ayah take nufi wajen bincike kafin daukar hukunci sai dai kila anmance da fadin أن فيكم رسول اللهabunda yake nufi shine muddun annnabi na nan to ba mai yanke hukunci sai shi. Yanxu da bayanan wa zaa tuntuba gama garin mutane? To malamai sune magada annabawa su zaa tunyuba da masu mulki kamar yadda ya tabbata a shariah.

LALLAI BA SHAKKA

Idan akayi bincike aka tambayi wannan corper shin kasan waye Muhammad? shin kasan wacece Amina ya amsa cewa ya sansu ya san kimar su awajen Musulmi hukunci zai hau kanshi amma ba na kisa ba har sai an sake tambayershi me yasa ko kuma wanne Muhammad kake nufi idan yayi ikirarin ganganci to na take zaa fille wuyamshi ko da alkali ko babu. Wannan shine hukuncin mai zagin Manzo kuma Allah ya laanceshi ya tsine mishi albarka.

SAKAMAKON HAKA

Abuida mutanen Funtua suka yi na kona chochi da kwashe dukiya da tafa hankalin alummah da sa su guje guje zalunci ne suka yi ba shakka kuma wuce gona da irine. Kuma jahilci ne Allah rabamu da jahilci.

Wannan ba bakon abu ba ne a Funtua saboda ga na garinsu, sun saba su yi kone-kone da zarar Musulmi ya fadi zabe su yi ta sace sacen dukiya. Wannan zai nuna maka cewa akwai bukatar malamai na Funtua su kara himma wajen ilmantar da mutane addini mai zurfi. Kuma su kaucewa sanar da gama garin mutane kalamai na motsa rai akan Mimbari. Mimbari amanar Manzo Allah ce, duk wanda ya hau dole ya isar da ita dai dai ko a sauko da shi.

Kai kuma mai kashe Yasir kar ka fasa. Dan dama mun dade muna son gane hakikanin masu kashe mana malamai da dalibai.

Yasir Ramadan Gwale
03-04-2014

No comments:

Post a Comment