Saturday, September 28, 2013

KANO TA DABO TUMBIN GIWA: Ko Da Me Ka Zo Ka Fimu!!!

KANO TA DABO TUMBIN GIWA: Ko Da Me Ka Zo Ka Fimu!!!

Kirarin da ake yiwa jihar Kano a baya shi ne "KANO TA DABO TUMBIN GIWA, KO DA ME KA ZO AMFIKA" wannan shi ne kirarin da duk mutumin kano yake alfahari da shi a baya, wanda kwanci tashi wannan kirari yana neman zama ba gaskiya ba. Domin idan ka kalli jihar Kano da Kanawa sai kaga da dama anzo Kano amfi Kanawa komai, abin da yake nuna wannan kirari ba gaskiya bane. Akwai misalai da yawa akan haka.

Abu na farko, ka dauki batun OTAL, kafatanin  Jihar Kano Otal guda daya ne wanda zaka iya kiransa Otal na fitar kunya. Wannan otal shi ne TAHIR GUEST PALACE, kusan idan ka dauke otal din Tahir duk sauran otal da suke Kano kodai sun dade a sume, ko sun mutu, ko kuma su ba masu raiba kuma su ba matattatu ba. Mu dawo batun Tahir, wannan Otal na Tahir, bako ne dan kasar Labanan yake mallakarsa, ko shakka babu abin farinciki ne da alfahari ace wani ya zo garinmu ya bude harkoki na kasuwanci dan tattalin arzikinmu ya bunkasa. Haka kuma, bayanai sun nuna cewa a kullum Tahir na samun kudi a kalla Naira Miliyan guda daga hannun jami'an gwamnati ciki da wajen Kano da suke yada zango a otal din, kaga a wata yana samun Miliyan Talatin kenan, wannan lissafin yana fin haka ninkim ba ninkim a wasu lokutan wani zubin kuma akan samu ragi.

Ka shiga Tahir ka gani abin da ke faruwa a cikinsa. Su waye ma'aikatan Otal din tun daga Junior Staff har zuwa Senior Staff. Wallahi galibin ma'aikatansu daga Arnan Jos sai Katafawa da sauran 'yan Kudancin Kaduna, idan kaga Bahaushe mutumin cikin birnin Kano bai wuce Direba (Mai tuka Mota) ko kuma mai wankin takalmi ko mai gadi da wankin mota ba, wadannan su ne galibin aikin da 'yan Kano suke yi a cikin Otal din! Shin babu 'yan Kano din da zasu iya sauran ayyukan ne? Ina wadan da hakkinsu ne su kula da harkar daukar ma'aikata a kamfanoni? Mun sani dokar kasa ta ce duk wani kamfani da zai bude a wata jiha to ya zama wajibi ya dauki "Personnel Manager" dan asalin jihar, amma ka je ka bincika ba wai Tahir kadai duk wani Kamfani da yake a Kano indai na baki ne to tabbas Personnel Manager ba dan Kano bane. Shin bamu da wannan masaniyar dokar ne?

Wani abin ban sha'awa kuma da takaici, shi ne gwamnatin da ta gabata ta Malam Ibrahim Shekarau ta yi yunkurin samar da katafaren Otal "Five Star" a Lamba wan (No 1) Ibrahim Taiwo Road inda yanzu ake kira Governors College. Abin takaicin shi ne wasu 'yan gaza gani suka je suka samu Mai martaba sarkin Kano suka fada masa cewar a dakatar da Gwamnati daga gina wannan Otal mai hawa 12 ko 15, wai a cewarsu baki wadan da ba 'yan Kano ba, zasu dinga zuwa suna kalle asirin cikin Birnin! Wallahi wannan shi ne abinda aka je aka gayawa mai martaba sarki, aka fada masa karya da gaskiya akan lallai a dakatar da gwamnati daga samar da wannan otal din. Yanzu zance ya zama sai labari.

Duk lokacin da za'a yi wani gagarumin bikin da baki za su zo Kano to a wannan ranar dakunan Otal na alfarma karanci suke yi. Domin idan ka zare Tahir da Royal Tropicana wanda shima yana daga cikin Otal din da ya suma. Sai wanne kuma? Duk sauran 'yan rakiya ne. Ita kanta gwamnatin Malam Shekarau da ta gabata anyi ta matsa mata lamba akan ta gyara Otal din Magwan yadda zai yi daidai da zamani ya samarwa da gwamnati da kudin shiga, gwamnatin ta yi jan kafa sosai akan batun, sai daga bisani aka so yin aikin kuma lokaci ya yi halinsa, wannan gwamnatin kuma yanzu haka ta mayar da Otal din makaranta kamar yadda ta mayar da Lambawan Ibrahim taiwo Road. Haka shima, Otal din Daula dake kan titin Murtala Muhammad shima ance ya zama Makaranta. Allah ya sakawa maigirma Gwamna da alheri lallai muna da bukatar karin makarantu bila adadun a cikin birni da kauyukan Kano. Amma lallai Kano na da bukatar dakunan kwanan baki da ake kira Otal, sannan kuma na bukatar kudin shiga. Wannan fa Otal kenan kadai.

Abu na biyu, shine kamfanonin Kwarori da sinawa 'yan chana da Indiyawa, ka je kabi kididdigar wadan da suke aiki ka tuntubi ma'aikatan kaji me ke faruwa a cikinsu. Dan chana arne a garin Kano zai hana Bahaushe Musulmi dan Kano zuwa Masallacin juma'a saboda keta da karya doka dan yasan babu abinda za ai masa. Da yawan wasu ma'aikatan kamfanuka sallah AZAHAR suke yi ranar juma'a saboda ba'a basu damar zuwa masallaci. Ina 'yan Kano da masu kishin Kano? Ina kungiyoyin kare hakkin Bil-Adama? Shin wannan ba cin mutuncinmu bane a addinance da 'yan kasance? Amma saboda su ma'aikata ana yi musu barazana da cewa ga mutane can a bakin get suna neman a daukesu aiki, duk wanda yaga ba zai iyaba ya kama gabansa, dole suke hakura saboda tsoron talauci da subucewar dama. Bayaga wannan ka tambayi yadda ake cin zarafin ma'aikata, dan chana ko Indiya ko kwara zai takarkare ya gallawa ma'aikaci mari akan abinda bai kai ya kawo ba, sai dai yayi Allah ya isa a zuci, ko abokan aikinsa ba zai iya sanarwa ba, saboda tsoron zai iya rasa aikinsa da yake ciyar da iyalansa da shi.

Akwai wani kamfani da na sani yanzu haka yana cin karensa babu babbaka a Kano. Asalinsa a jihar Edo ko Imo ya fara yada Zango, amma saboda jihohin sun san me suke suka ce lallai su zasu bashi Personnel Manger kamfanin yaki yarda. Akan haka ya yarda yayi asarar kudin da ya kashe wajen yin gine-ginen matsuguni, ya wanke kafa ya zo Kano, yanzu haka yana cin akuya ce ko karensa babu babbaka, saboda ya samu jahilai gidadawa wadan da basu san inda yake musu ciwo ba. Su dai bukatarsu cikinsu da farjinsu. Wadannan fa, baki ne 'yan kasashen waje suke gallaza mana da cuta mana a cikin garuruwanmu, da muke ihu da kirari mun fi kowa. Sannan kuma akwai  'yan kasa kudawa abokan zamanmu, Inyamurai da sauran kabilu wadan da suka mayar da kafatanin kasuwanninmu nasu, idan kaga Bahaushe to ko dai dillali ko dan kamasho ko dan kayi nayi. Allah ya sawwake! Zan cigaba In Sha Allah.

Yasir Ramadan Gwale
28-09-2013

No comments:

Post a Comment