Thursday, September 19, 2013

RIKICIN BOKO HARAM: Ana Rufe Kura Da Fatar Akuya!!!

RIKICIN BOKO HARAM: Ana Rufe Kura Da Fatar Akuya!!!

Tun lokacin da aka bayar da sanarwar ayyana dokar ta baci a jihohin Borno da Yobe da kuma Adamawa adadin rayukan da suke salwanata yake karuwa musamman a jihar Borno. A zatanmu ayyana dokar ta bacin nan da shugaban kasa ya yi zai kawo saukin lamura, adadin rayukan da suke salwanta zasu ragu, amma sai akasin haka ne yake faruwa. Tun da sojoji suka yiwa Jihar Borno tsinke kusan kullum labarin asarar rayukan da ake bayarwa sun shallake hankali da tunani, wani abin mamaki da daure kai shi ne yadda ake bayar da rahotannin cewar su 'yan Boko Haram suna yin bazata ta hanyar amfani da kayan sojoji su je su farwa farar hulu su salakasu. Ko shakka babu wannan babban abin tashin hankali ne da kuma daure kai. Ta yaya rundunar tsaron jihar Borno zasu iya gamsar da mu cewar wadan da ake bada rahotannin sun sanya kayan sojoji sun kaiwa fararan hula farmaki 'yan ta'adda ne ba sojojin gaskiya bane?

A baya duniya ta shaida yadda sojoji suka shiga garin BAGA inda suka kashe darururwan mutane sannan suka sanyawa dubban gidajen jama'a wuta babu gaira babu dalili, sannan daga bisani bayan karairayin kare hakkin bil adama da kungiyoyi da daidaikun mutane suka dinga yi gwamnati ta bayar da sanarwa kafa kwamatin da zai binciko gaskiyar abin da ya auku. Inda babu jimawa rundunar tsaron suka ce 'yan Boko Haram ne suka batar da kama wajen sanya kayan sojoji suka aikata wannan mummunan aikin ta'addancin! Kuma shi kenan har yanzu zancen ya sha ruwa babu wanda ya kuma daga shi, zancen rahoton kwamitin da shugaban kasa ya kafa yabi iska, har yau babu wanda aka kama ko aka tuhuma da wannan mummunan aikin ta'addanci, an kashe banza an gudu.

Sannan kuma, Tun bayan harin garin BAGA kusan duk sanda za'a bayar da rahotan kisan fararen hula, sai ace wasu masu sanye da kayan sojoji sun kashe mutane 10 ko 20, ko 30. Wanda yanzu abin ya fara neman shallake hakali da tunani inda a cikin wannan makon aka ce wai wasu  'yan Boko Haram sanye da kayan sojoji sun tare hanyoyi suna yayyanka mutane tare harbesu har lahira, a yayin da a gefe guda kuma aka bayar da rahotannin an kashe 'yan Boko Haram kusan 150 wanda wannan adadi ne mai girman gaske. Al'amarin akwai daure kai da rikitarwa! Shin da gaske ne wadan da sojojin suke kashewa 'yan Boko Haram ne? Shin da gaske ne su 'yan Boko Haram ne suke yin bazata da kayan sojoji suke kashe jama'ar da basu san hawa ba basu san sauka ba? Wadannan sune tambayoyin da ya kamata mu yi.

Bisa ga dukkan alamu, duk irin wannan batarnaka da ke faruwa a jihar Borno ana rufe kura da fatar akuya ana sauya akalar gaskiya. Amma hakika munyi Imani da dukkan Kaddara mai kyau da marar kyau, duk abubuwan da suka wakana masu kiyayewa sun kiyaye a cikin takardun da ruwa baya shafe zanens. Lokaci zai zo komai tsowon zamani da gaskiyar abubuwan da suka faru zata bayyana. Fatanmu Allah ya cigaba da karemu da kariyarsa, ya yi mana garkuwa da garkuwarsa. Su kuma wadannan 'yan ta'adda Allah ya tona musu Asiri ya wargaza shirinsu da makircinsu. Allah ka bamu lafiya da zama lafiya.

Yasir Ramadan Gwale
19-09-2013

No comments:

Post a Comment