Thursday, September 19, 2013

MALAM SALUHU SAGIR TAKAI: Mai Kamar Zuwa Kan Aika!!!

MALAM SALUHU SAGIR TAKAI: Mai Kamar Zuwa Kan Aika!!!

Malam Saluhu Sagir Takai mutum ne da ba shi da bukatar wani dogon ta'arifi wajen al'ummar jihar kano. Malam Saluhu tun yana shugaban karamar hukumar Takai al'umma suka shaida nagartarsa da kwazonsa da kuma jajircewarsa wajen ganin anyi gaskiya da sanya abubuwa a muhallansu, wannan ce ta sanya ko a shekarar 2001 lokacin da tsohon shugaban kasa cif Olishegun Obasanjo ya kawo ziyarar aiki a Kano lokacin Gwamna Rabiu Musa Kwankwaso karamar Hukumar Takai aka kai Obasanjo domin ya ga ayyukan raya kasa da shugaban karamar hukumar yayi duk kuwa da kasancewarsa dan jam'iyyar Hamayya. Wannan kadai ya isa ya nuna maka nagartar wannan dan tahaliki, haka kuma abokan aikinsa sun shaida tare da yabawa da irin gaskiyarsa da rikon amanarsa.

Jama'a da dama sun shaida lokacin da ya rike kwamishinan Kananan Hukumomi da kwamashinan Ruwa, karkashinsa aka samar da madatsar ruwa mafi girma a fadin Najeriya, har ya gama ba'a zargeshi da wata al'mundahana ko batar da sawun gaskiya ba. Malam Saluhu Sagir Allah ya sa mutum ne mai tsantseni da takawa ga kuma tsoron Allah, wannan shakka babu zato ne na zahiri wadan da dukkan jama'ar da suka yi Mu'amala da shi sun kyautata masa wannan zatan, ya alkinta amanar dukiyar da aka bashi, har yanzu ba'a sameshi da almubazzaranci ko barnata dukiyar al'umma ba.

Haka zalika ko a lokacin da ya yi takarar Gwamna a shekara ta 2011, anga irin shaidar da al'umma suka yi masa domin, ya gudanar da yakin neman zabe mafi tsafta a tarirhin siyasar Kano. Babu kalamai na tashin hankali, babu zage-zage ballantana zubar da jinin wadan da basu ji basu gani ba da sunan Bangar Siyasa. Allah shi ne mai bayar da Mulki a Lokacin da ya so kuma ga wanda ya so, Allah cikin hukuntawarsa bai kaddara Malama Saluhu ya samu Nasarar zama gwamna ba a zaben da ya gabata. Bisa irin waccan Nagarta tasa da kuma tsantseni da kokarin kamanta gaskiya tasa ta sanya muke ganin ya kamata jama'ar kano su bashi dama domin tabbatar da zaton alkhairi da aka yi masa.

Alhamdulillah, Batun ayyukan raya kasa wannan ba bakon abu bane a wajen Malam Saluhu Sagir Takai, domin da irin shawarwarinsu ne Gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau ta aiwatar da kyawawan ayyukan raya kasa a fadin jihar kano. Tun daga asibitoci da tituna, da makarantu da ayyukan yi. Ta bangaren Inganta harkokin Addinin Musulunci a Gwamnatance wannan abu ne da tun farko aka yi masa shaida akai, akan haka ne ma wasu ke zarginsa da cewa ya cika riko da addini, wanda wannan kyakykyawan zato ne ba zargi ba a wajen duk wani mai hankali da sanin ya kamata.

Lallai Jihar Kano tana bukatar Jan Namiji gwarzo jarumi mai kokari da tsantseni da takawa da sanin ya kamata. Malam Saluhu Sagir Takai Allah ya amince ya zama Gwamnan Kano a 2015.

Yasir Ramadan Gwale
Shugaban Kungiyar, Takai Youth Mobilisation.
yasirramadangwale@gmail.com
19-09-2013

No comments:

Post a Comment