Friday, September 20, 2013

Anya Gwamnonin Arewa Suna Da Gaskiya Kuwa?


ANYA GWAMNONIN AREWA SUNA DA GASKIYA KUWA?

Halin da Arewa ta samu kanta a ciki a wannan mawuyacin lokaci, hali ne da babu wanda yake bukatar a yi masa bayanisa. Irin wannan mummunan yanayi da Arewa ta samu kanta a ciki bamu ta'ba shiga wani irin yanayi mai kama da haka ba a baya. Zaman lafiya ya kauracewa jihohi da dama, harbe-harben bindigogi da karar tashin bomabomai sun zama abu na yau da kullum, kusan yanzu zamu iya cewar da dama a Arewa an saba da jin karar harbin bindiga da karar fashewar Bom. Abubuwa na ta'addanci sun gama kankama a kusan kafatanin jihohin Arewa, ko ina batu ake na sukurkucewar al'amuran tsaro. Wannan rashin tsaro gwamnonin Arewa suka saya da kudinsu, aka kuma sayarmusu. Domin tun da aka samu gwamnonin da suka dinga Amfani da 'yan Banga suka saya musu Makamai dan farwa duk wanda suke jin zai iya shiga gabansu, al'amuran tsaro suka lalace. Misali na gwari-gwari shi ne yadda tsohon Gwamnan Borno Ali Shariff yayi amfani da ECOMOG ya saya musu makamai su ba jami'an tsaro ba, wanda wannan tsohon gwamna yana da hannu dumu-dumu akan halin da jihar Borno ta samu kanta a ciki na lalacewar al'amuran tsaro.

Haka zalika, idan muka kalli gwamnonin nan bakwai masu tayar da kayar baya a jam'iyyar PDP ya isa ya nuna mana rashin gaskiyar Gwamnonin Arewa. Su wadannan gwamnoni sun hada kai tun suna su hudu har suka zama Biyar daga baya suka zama bakwai dan abinda suka kira kwatowa kansu 'yancin da suke ganin Jam'iyyarsu tana neman danne musu. Labarin sabatta juyattan da ake yi tsakanin wadannan gwamnoni da suka bijirewa jam'iyyarsu da kuma shugabancin jam'iyyar karkashin Bamanga Tukur kusan ya zama ruwan dare gama duniya, duk wanda yake bibiyar al'amuran da suke faruwa yana da masaniyar abubuwan da suke faruwa da wadannan gwamnoni. Wadannan bijirarrun gwamnoni sun hada kai suka nemi tsayar da kasarnan cik domin nemawa kansu mafita. Kusan kullum Mitin ake a Abuja fadar gwamnati domin tattauna yadda za'a shawo kan wadannan bijirarrun gwamnoni. Wannan abu ne da yake a fili cewa suna yi ne dan biyan bukatar kashin kansu, kuma dole aka tsaya ake sauraren yadda za'a biya musu bukatunsu.

Daga cikin bukatun da wadannan gwamnoni suke son a biya musu bayan sallamar shugaban jam'iyyarsu Bamanga Tukur, har da kiran da suka yiwa shugaban kasa na kada ya kuskura ya tsaya takarar sake neman shugabancin kasarnan a zaben 2015 mai zuwa. Anan ne zaka fahimci rashin gaskiyar wadannan gwamnoni, domin idan muka koma baya sun fito suna ihun cewa Jam'iyyar tana da tsarin karba-karba, wanda suka ce dole a mutunta shi domin yarjejeniya ce da aka yi a Jos a shekarar 2005, kuma shi wannan shugaban Goodluck Jonathan ya halarci wannan yarjejeniya, amma ya kekasa kasa yace shi sam bai san zancen ba, a zaben 2011 da ya gabata, kuma gwamnonin suka mara masa baya. A takaice suka yi yarjejeniya shugaban ya karya musu yarjejeniya. Ban sani ba ko batan basira ne ya sa suka ce wai bayan da shugaban ya karya waccan yarjejeniya, suka sake kulla wata yarjejeniyar da shi akan cewa karo daya kawai zai yi, inda shima da bakin shugaban ya amsa cewa Karo daya zai yi! Wanda daga bisani Kakakinsa yace Shugabanfa da wasa yake yi. Tayaya mutumin da kuka yi yarjejeniya ya karya zaku sake kulla wata yarjejeniyar tare da shi? Watakila ko nine ban fahimci al'amarin ba.

A zaben fitar da gwanin da aka yi na PDP tsakanin Atiku dan Arewa da Goodluck Jonathan, wadannan gwamnoni suka tsaya kai da fata cewa sai keyar Atiku ta taba kasa a zaben fitar da gwanin. Domin kuwa Gwamnan jihar Adamawa Murtala Nyako da kansa ya tsaya a bakin akwatin jiharsa akan dole daliget na jihar su zabi Jonathan su bar dansu Atiku. Haka zalika sauran gwamnonin babu wanda bai yiwa Jonathan Kamfe a sarari ko a boye ba, akan ganin shugaban ya kai labari. Haka suka dage sai da shugaban ya samu kaso 25 da hukumar zabe ta yi tanadi a kowacce jiha. Babu gwamnan da bai yi kokarin Jonathan ya kawo wadannan kuri'u ba. Yanzu kuma abin mamaki wai sune suka fito suke kalubalantar abinda suka ce sunji sun gani gara tsintacciyar mage akan magen gida.

Sannan kuma wannan tayar da kayar baya da gwamnonin suke yi da ta kusa tsayar da kasarnan cik saboda sun hade kansu, zai tabbatar maka da cewa da sun hada kai su sha tara ko sha bakwai akan cewa tilar al'amuran tsaro su kyautata a Arewa gabaki daya, kana jin zamu kawo yar yanzu ana fama da tashe-tashen hankula? Kanajin da sun hada kai suka ce Tilar a tayar da kafadun masana'antun da suka durkushe hakan ba zai yuwu ba? Kanajin da sun hada kai suka ce tilar a aiwatar da aikin yashe kogin kwara da marigayi YarAdua ya faro za'a tsaya? Wannan ya kara tabbatar mana da gangan duk abinda suke faruwa na sukurkucewar tsaro, da karyewar tattalin arziki suke faruwa, wallahi idan wadannan gwamnoni sun so sai al'amura sun daidaita, amma da yake su gaba ta kaisu suna samun fa'ida da tashin hankali babu abinda ya shafesu. A kalla ace gwamnoni Goma suka hade kai suka ce sai shugaban kasa ya gyara al'amuran tsaro da suka sukurkuce lashakka sai lamura sun kyautata, amma saboda ba bukata bace ta kashin kansu shi yasa muke cigaba da kasancewa cikin zullumi a kullum ranar Allah.

Jami'o'i suna cigaba da kasancewa a garkame 'ya 'yan talakawa na gararamba da watangaririya babu karatu babu aikin yi a cikin unguwanni. Kasuwancin yana kara komawa baya a kullum, Fashi da makami kullum yana karuwa, fashi na rainin hankali domin sai a shafe awanni sama da biyu ana fashi, kuma a gudu bayan ankwashi makudan kudi ba tare da anga ko kurrar 'yan fashin ba. Lallai da ace da gaske wadannan gwamnoni suna kishin Arewa da suke tinkaho dole a tsaya a sauraresu a kuma biya musu bukatunsu, dan fitar da Arewa daga cikin halin da ta ke na bacin tafarki.

Lallai Muna kira ga gwamnoninmu da suji tsoron Allah su hade kansu wajen dawo mana da martabarmu da kimarmu da ta zube warwas a idan duniya. An rainamu saboda bama iya warware matsalolinmu da kanmu, mun kasa fahimtar ina muka dosa, an jahiltar da mu, an shiga gabanmu ta ko ina. Lallai suji tsoron Allah su hada kai wajen kawo karshen wannan tashe tashen hankula da suke faruwa.

Yasir Ramadan Gwale
20-09-2013

No comments:

Post a Comment