Thursday, August 1, 2013

ME YA HANA 'YAN SHI'AR NAJERIYA ZUWA QUDUS NE HAR YANZU?


ME YA HANA 'YAN SHI'AR NAJERIYA ZUWA QUDUS NE HAR YANZU?

Duk shekara ya zama addini a wajen 'yan SHI'AH su fito kan tituna da tutoci da kwalaye rike suna rera wakokin nuna cewa Masallacin Qudus nasu ne, kuma sai sun je har Qudus din sun kwato kayansu daga mamayar da Yahudawan Israela suka yi masa. Shekaru masu yawa El-Zakzaky yake ta wahalar da matasa da mata da yara cewa wai zasu je su kwato masallacinsu, tun daga lokacin da suka fara wannan harmagazar har yau basu taba tsallaka kan iyaka ba dan zuwa Aqsa ba. Amma watakila ina zaton ko basu san hanya bane. Bari na yi musu kwatance tunda sun shahara da yin tattaki a kasa, hanyoyi ne guda biyu daga Najeriya zuwa Masallacin Qudus ko Aqsa, ko dai su bi ta Nijar, su keta saharar dake Agadez su shiga ta Arlit a Algeria su bi ta Tamariset su keta hamadar Algeriya sannan su isa har Libya daga nan su dangana zuwa birnin Benghazy dake da iyaka da kasar Masar daga nan sai su shiga mashigar nan da ake kira RAFAH sai Qudus; idan wannan hanyar ta yi musu tsawo su bi ta Iyakar Najeriya da Chadi, su keta kasar gaba daya su shiga ta El-fashir a Sudan daga nan su dangana Nehud kan iyakar Sudan da Masar, suna shiga Masar sai mashigar RAFAH, daga Najeriya duk wanda zaiyi tattaki zuwa Qudus wadannan su ne hanyoyinsa. Idan basu san hanya ba ga shi nan mun yi musu kwatance, Idan suka fita a gobe kafin bad'i war haka tuni sun Isa Qudus, kaga daga nan sai su fara gwagwarmayar dawo da Massalacin Qudus.

Yahudawa na can na kashe Musulmi a Palastine babu dare babu rana, amma Jahilan suna Gyallesu suna cewa zasu kwato masallacin Qudus. Me ya hana IRAN kai sojojinta QUDUS don taimakon Palasdinawa da kuma kwato Qudus kamar yadda suka tura sojojin su kasar Syriya suna kashe Musulmi da basu san hawa ba, basu san sauka ba, suna rurrusa masallatai tun wadan da Sahabbai suka gina, amma saboda rashin kunya, makirai sai su ce ai IRAN ke baiwa 'yan HAMAS makaman da suke yakin ISRAELA, mu duk wannan babarodon ba zamu gane ba, muna son kamar yadda aka tura sojan IRAN yankunan QUSAYR a SYRIA muna jiran muga sojan IRAN a yankunan GHAZZA da WEST BANK da sauran yankunan Palasdinawa da Israela ta mamaye.

Kuma daman su 'yan SHI'AH sun shara da 'batar da sawun tarihi, domin kuwa shi kansa wannan hoton da suke yawo da shi mai kubba ruwan zuma ai ba shine Majid Aqsa ba, Massalacin Quds na ainihi yana da Bakar Kubbah ne ba wannan bane mai ruwan zuma da shi'ah ke yawo da shi suna san jirkita tarihi su rudi jahilai wadan da basu fahimci yadda lamarin yake ba.

Mu MUSULMI mun san da cewa Masallacin AQSA daya ne daga cikin Manyan masallatan MUSULUNCI guda uku da Manzon Allah ya ce su kadai ne za a iya nikar gari domin tafiya ziyara, kuma mun kyautata zato ga ALLAH cewa wannan Masallaci ko ba da'de ko bajima sai wannan Masallaci ya koma mallakar Musulmi amma ba 'yan SHI'AR da ake sarrafawa daga TEL AVIV da NEW YORK ba, 'yan shi'ar da suke yiwa su NETANYAHU aiki wajen kashe dubban al'ummar Musulmi babu gaira babu dalili.

Yasir Ramadan Gwale
01-08-2013

1 comment:

  1. Mai za su je su yi?!! Ai daman karya ce kawai suke yi don yaudarar Alumar Musulmai da ba su fahimci asalin addinin Shi;la linla ta dosa ba!! Sai kawai Hayaniya da bankwaura!!

    ReplyDelete