Sunday, August 18, 2013

Gabas Ta Tsakiya: Anya Za A Zauna Lafiya Israela Na Kallo?

GABAS TA TSAKIYA: ANYA ZA'A ZAUNA LAFIYA ISRAELA NA KALLO?

Zai yi wahala a samu zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya alhali kasar Israela na wajen. Kada ka ji da wai duk wata rikita rikita da ke faruwa a kasashen larabawa akwai hannun Israela da uwar gijiyarta Amerika a ciki. Sanin kowa ne cewa Israela wata tsokar Nama ce a jikin Amerika, wacce Amerika ba zata iya wani amfani ba tare da aikin wannan tokar naman ba, zaka iya kwatanta ta da "zuciya", a takaice ana tafiyar da harkokin Siyasar Amerika ne kai tsaye daga Warshington da New York kamar yadda ake baiwa Amerika umarni kai tsaye daga Tel Aviv su karba ba tare da wata tirjiya ba, su biyun sashinsu yana taimakawa sashi. Israela ba zata taba bari a zauna lafiya ba a yankin gabas ta tsakiya, domin kuwa suna da masaniyar cewar Indai kasashen Larabawa suna zaune lafiya, tilar ayi maganar samar da 'yantacciyar kasar Palasdinu, domin kaucewa wannan batu da baya yiwa Tel Aviv da Warshington dadi, ya sa dole su shirya yadda yankin zai yamutse da rikici da hayaniya. Sannan su kuma rarraba tsakanin kasashen a siyasance.

Da farko idan ka kalli kasar Siriya, kusan shekara biyu kenan ana yin abu guda daya, mutum daya dan isaka ya zama masifa! Wato abin da yake faruwa a Siriya shine, su Turai da Amerika da Israela basa son rikicin Siriya ya zo karshe nan kusa, haka kuma, basa son ko da rikicin ya kare a samu wanda yayi galaba akan wani, Basa son Assad dan Ta'adda ya samu Nasara duk da suna tare da shi a bayan fage, sannan kuma basa fatan Free Syrian Army su sami nasara akan Assad, domin a tsarinsu kamar kware musu bayane tunda sun ayyana goyon bayansu a garesu, wanda goyon baya ne mai cike da yaudara, da jan kafa. Duk da wannan abin da yake faruwa a Siriya Israela da Amerika sun gwammace Assad ya cigaba da kasancewa a matsayin shugaban Siriya domin ko babu komai suna da masaniyar ba zai tayar da batun tsaunukan Golan da Israela ta mamaye ba; sannan suna tsoro kada su mara cikakken goyon baya ga FSA su kafa gwamnati a samu mai kishin addinin da zai saba da manufofin Israela a gabas ta tsakiya, wanda wannan shine hakikanin abinda zai faru, amma idan banda haka awanni ashirin da hudu sunyi yawa Amerika ta hambarar da Assad.

Na biyu kuma, idan ka kalli Masar, suna tsoron samun Nasararsar Muhammad Mursi a matsayin halastacce shugaban Masar bisa doron Dimokaradiyya, wanda hakan babban koma baya ne ga Israela. Domin ba tare da wani boye boye ba, Mursi ya nuna baya tare da Israela, kamar yadda tsohuwar Gwamnatin Sadat da ta Mubarak suka d'asa da Isreala, dan haka suka yi dukkan mai yuwuwa dan kifar da gwamnatinsa. Kuma kifar da gwamnatin Mursi ba shi kadai ne abinda zasu yi su koma su zauna ba, zasu kasa su tsare su tabbatar kasar ta yi rincabewar da duk wani mai kishin Addini bai samu irin damar da Mursi ya samu ba. Dan haka duk wannan abin da yake faruwa wanda ake amfani da su Sisi da Bublawai da ElBaradie an riga an gama shirya shi dan rikita kasar. Allah ya kawowa Misrawa dauki cikin kaddararwarsa.

A gefe guda kuma sauran kasashen Larabawa suma suna bayar da nasu taimakon wajen ganin, Masar bata samu Nutsuwar da zata baiwa Ikhwan dawowa kan karagar Mulki ba, domin suma suna da masaniyar cewar Matukar MB suka samu nasarar gwamnati a masar kashin kasashen Saudiyya, da Kuwaiti, da Qatari, da Bahrain, da Abu Dhabi ya bushe, dole guguwar siyasa ta kada a kasashen, abinda ba zai taba yi musu dadi ba, dan haka ba zai taba yuwuwa ba su nade hannu su kyale Ikhwan ta samu Nasara a Masar! Allah ya basu Nasara.

Sannan kasashen Gabas ta tsakaiya gabaki dayansu ba suda gaskiya. Musamman akan siyasarsu ta Diplomasiyya wadda ake kira Foreign Policy, domin dukkansu babu kasar da take da wata manufa ta Allah da kuma kare addinin Allah a bisa hakikanin lamura, ko da akwai manufar addini to siyasarsu ta kashin kansu ta rinjayi siyasar Addini. Wannan wani al'amari ne mai girma kuma mai fadi! Watakila wani ya zargi Alakar wadannan kasashe da Amerika, Eh kana da 'yancin zarginsu akan alakarsu da Amerika, amma abu ne sananne cewar Amerika tana da bukata a gabas ta tsakiya, kuma sannan tana da kudi a gindinta; suma haka kasashen suna da bukata ga Amerika domin suna da haja da suke samun kudi suke juya siyasar Khalij yadda suka ga dama.

Babu yadda Israela zata kasa wanzuwa a yankin gabas ta tsakiya matukar Akwai Amerika. Idan kana bukatar kawar da kasar Israela daga doron kasa sai ka tabbatar ka share Amerika sannan ka iya kawar da Israela, amma duk wani abu da ba wannan ba, to sunansa dodo-rido, anan zaka zargi kasar IRAN kasan cewar duk ihun da suke yi karyar banza ce akan Israela babu wani abu da zasu iya yi, hasalima bakinsu daya da Israelar wajen rikita lamura da kuma rikita kasashen sunni da sanya musu rashin Nutsuwa, haka kuma, duk da gazawar kasashen Sunni sunyi rawar gani a wasu fannoni sun kuma dirka abin kunya a wasu fannonin, amma dai sunfi IRAN nesa ba kusa ba.

Waye zai iya yakar Amerika? A wannan zamani da muke cikin karni na 21 karfin soja ya zama zancen banza. Yanzu lokacin karfin soja ya wuce, domin ana aiki da karfin fasaha ne, Soja yana zaune a cikin bairiki zai tura jirgin sama mara matuki ya kashe duk mutanan da yaga dama ya dawo, kaga duk rawar daji da tsalle-tsalle na soja sun zama zancen banza, domin abokin karon nasa ma baya ganinsa amma shi yana hangoshi. Babu wata kasa da zata iya yakar Amerika alhali bata da iko akan Bankin Duniya, da IMF da Majalisar Dinkin Duniya da kuma NATO. Babu wata kasa da zata iya karawa da Amerika ta yi galaba akanta matukar bata da ikon mallakar wadannan janibai da muka zayyana. Amerika kuwa na da iko akansu sama da kowacce kasa. Ko Rasha da take ganin sunyi kafada da Amerika sai dai su yi kare jini biri jini.

Fatanmu shi ne Allah ya zama gatan bayinsa na gari a duk inda suke. Allah ka taimaki Addinin Musulunci da masu taimakonsa a zahiri da fake. Allah ka Amintar da mu a cikin kasashenmu.

Yasir Ramadan Gwale
15-08-2013

No comments:

Post a Comment