Saturday, August 24, 2013

El-Zakzaky Ne Babbar Matsalar Tsaro A Najeriya!!!

EL-ZAKZAKY NE BABBAR MATSALAR TSARO A NAJERIYA!!!

Sanin kowa ne cewar ana matukar fama da matsaloli na tabarbarewar tsaro a Najeriya musamman Jihar Arewa inda Musulmi ke da rinjaye. Labaran kashe-kashe da tashin hankali da barazanar salwantar rayuka da dukiyoyi a kusan dukkan jihohin Arewacin Najeriya ba wani sabon abu bane, musamman a wannan mawuyacin lokaci da muke ciki, wanda al'amura kullum sai kara jagulewa suke yi, zubar da jini sai karuwa yake yi, a kullum sai yanka mutane ake yi kamar yadda ake yankan dabbobi a Abbatuwa. Kusan wannan matsalar ta shafi ko ina, yanzu ya zama babu wani waje da yake da Aminci a Arewacin Najeriya, domin tundaga Masallatai da gidajen jama'a da kasuwanni da guraran haduwar jama'a babu wani waje da bai taba samun barazanar tsaro ba, anbi mutane har cikin Masallaci suna Sallah an kashe su kuma WAI an tsere, ba'a kama kowa ba; haka zalika kasuwanni sun sha fama da tashin hankula iri-iri; haka ma, dai-dai kun mutane an sha binsu har cikin gidajensu a yankasu kamar awaki kuma a gudu ba tare da anga ko da kurar mutum ba. Duk wannan barazana da tashin hankali a Arewa ba bakuwa bace kusan idan ana sabo da barazanar tsaro irin wannan to zamu iya cewa wannan to zamu iya cewa an saba da ita.

Zance na gaskiya Barazanar tsaro mafi girma ga Musulmin kasar nan Shine wani mutum da ake kira Ibrahim El-Zakzaky. Hukumomin tsaro ya kamata su yi hattara kuma su shiga taitayinsu, su kuma san abinyi akan wannan mutum, da yake jagorantar tarin marasa Ilimi da wawaye da Talakawa da ba su da cin yau balle na gobe, ga tsananin jahilci. Tabbas Zazzaki barazana ne, domin ya tara mutane a karkashinsa basa yin aiki da umarnin kowa sai nasa, basa jin maganar kowa sai tasa, Shugabannin Siyasa da Sarakuna da Suhagabannin tsaro maganganunsu ba abakin komai suke ba a wajen mabiyan Zazzaki, domin basa karbar umarni daga garesu face abin da Zazzaki ya umarcesu. Bil hasali ma, suna ganin dukkan wadancan bangarorin shugabanni na al'umma a matsayin DAGUTAI, haka shima Zazzakin yana yin gaban kansa wajen bijirewa dukkan wani abu da yake doka ne a kasarnan gabansa gad'i.

Sanin kowane a Arewacin Najeriya, mabiyan Zazzaki basa bin dukkan wata doka da hukumomi suka sanya, walau dan kare dukiya ko kuma dan kare rayukan al'umma. Mabiyan Zazzaki suna karya doka kan su tsaye ba tare da tunin doka ta yi aiki akansu ba, kuma hukumomin tsaro da al'hakinsu ne su tsaya tsayin daka wajen ganin al'umma na bin doka da oda, amma sun zurawa mabiyan zazzaki ido suna yin iya shege da tsakar rana babu kunya babu tsoron Allah suna taka dukkan wata doka da aka sanya. Lallai muna kiran hukumomin tsaro da masu mulki da shugabanninmu, wajibi ne agaresu su takawa Zazzaki birki, akan irin wannan cin kashi da karan tsaye da suke yiwa dokoki. Kuma lallai hukumomi su sani cewar babu yadda za'a yi a zauna lafiya matukar wani bangare na al'umma an barsu suna iya shege da taka doka, hukunci baya hawa kansu. Lallai a kama tare da tuhumar dukkan wanda ya taka dokokin hukuma ko waye shi.

Haka kuma, sanin kowa ne cewar Zazzaki a Azumin da ya gabata ya saba da dukkan Musulmin kasarnan, domin ya dauki Azumi ba tare da iznin hukuma ba, ya kuma baiwa mabiyansa umarni suka bi umarninsa, duk da cewa al'haki ne na sarkin Musulmi ya bayar da sanarwar daukan Azumi ko ajjiyeshi. Amma zakzaky ya kekasa kasa ya yi kunnen uwar shegu ga bin umarnin fadar Sarkin Musulmi. Wannan karara yana nuna cewar Zazzaki zai iya umartar mabiyansa da dukkan abinda yaga dama, duk mutanan da yaga dama yana iya cewa a farmusu kuma ayi hakan, lallai ne hukumomi su ankara su san matakin dauka akan wannan mutum.

Muna gani duk kasarnan babu wani mutum da yake kiran jama'a su fito kantituna kwai da kwarkwata kamar yadda zakzaky ke yi. Zazzaky yana umartar mabiyansa da fitowa a duk lokacin da yaga dama, har da basu umarnin yin tattaki da kafa daga nisan gurare, wanda wannan karara ya sabawa HAKKIN BIL-ADAMA amma anaji ana kallo aka yi shakulatun bangaro da batunsa. Lallai wajibi ne jama'a su fadaka, su sani cewar dole ka kula da 'ya 'yanka wajen ganin basu bi wannan mutumin da yake halakar da su ba, yake raba su da IMANI na hakika, wajen cusa musu wani abu daban da sunan Addini. Sannan kuma, wajibin hukumomi ne su dauki tsauraran matakai akan Zazzaki domin samun zaman lafiyar al'ummar kasarnan. Rashin hakan kuwa jefa kasarnan ne cikin tashin hankalin da yafi duk wanda aka taba fuskanta a baya. Idan kunne yaji . . .!

Yasir Ramadan Gwale
23-08-2013

1 comment: