Wednesday, September 19, 2012

Ngozi Okwonjo-Iweala Ta Kasa Fahimtar Ma’anar Rashawa Da Cin-Hanci



Ngozi Okwonjo-Iweala Ta Kasa Fahimtar Ma’anar Rashawa Da Cin-Hanci

An shaida ma na cewa Dr Ngozi Okonjo-Iweala, ministar kudi kuma ministar da a ka dorawa alhakin habaka tattalin arzikin kasa, an horar da ita ne a Bankin Duniya domin yin jagoranci, inda har ta kai mukamin daya daga cikin manyan daraktocin bankin. Saboda haka za mu iya cewa ta fahimci ka’idojin da ke samar da jagoranci nagari. Abin kunya ne a ce ta na cikin gwamnatin da a ka sace Naira tiriliyan 2.6 ba tare da ta nuna kwarewarta wajen hana afkuwar hakan ba. Abin mamaki matuka ganin yadda Okonjo-Oweala ta amince ta jagoranci ma’aikatar da za a tafka irin gagarumar sata duk da irin tarbiya da horon da a ka ce ma na ta samu a bankin duniya. Amma wannan da alamu wannan shi ne dan-ba ga abinda Okonjo-Oweala ta sa gaba.

A ‘yan makonnin da suka gaba ta ne, ta fito ta shaidawa duniya cewa za ta iya jingina da kamfanonin man da rahoto ya kama da laifin wawure dukiyar kasar da ta kai tiriliyoyin Naira. A ta bakinta “mu na da burin cewa wadanda a ke kallo a matsayin sun aikata babban laifi za mu yi jinga da su, idan har su na son yin aiki tare da mu ta yadda za mu ba su dama su warware matsalar ta hanyar shigowa da shi.” Matsalar wannan gwamnatin ita ce irin ta Obasanjo, wato masu gudanar da ita sun mance da ma’anar kalmar almundahana. Kuma duk da cewa Okonjo-Oweala ta sami kwarewar mataki na duniya a bankin duniya, amma ta na karbar mukami a gwamnatin Jonathan sai ta koma ta zama tamkar kidahumar ’yar kauye.

A wajen ministar kudin, wasu daga cikin barayin ‘ba su tafka babban laifi ba’. Ba ta shaida ma na wacce sata ce ba babban laifi ba. Watakila satar Naira biliyan daya daga cikin Naira tiriliyan 2.6 ita ce ‘ba babban laifi ba’. Ko ma ta zama Naira miliyan 100? Ina iya tuna wani jami’in gwamnati da a ka yi zargin ya sace Naira biliyan uku, ya amsa a fusace ya na mai cewa, “Naira biliyan 2.5 ne kawai.” Shin irin wannan shawarar ta ke bai wa iyayen gidanta a bankin duniya? Abin mamaki ne ganin yadda ita ce wacce ta yi ritaya daga gwamnatin Obasanjo kan abinda bai kai wannan zama badakala ba, amma a yau ita ta nutsu da abinda ke faruwa. Abu ne wanda hankali ba zai dauka ba a ce ita ce har yanzu a cikin gwamnatin da a ke tafka badakala irin ta gwamnatin Jonathan.

Ba wannan kadai ba. Okonjo-Oweala, wacce ta ke kallon bashin Dala biliyan 32 a matsayin abu mai tsananin hatsarin da ba za a jure ba kuma ta jagoranci gwamnatin Obasanjo a 2006 a ka biya Dala biliyan 18, inda a ka yafe Dala biliyan 32 don ceto kasar daga kangin bashi, a yau kuma ita ce ta ke cewa bashin Dala biliyan 45 ba komai ba ne na damuwa (bayan fa shekara shida kacal da yafe Dala biliyan 32). Shin akwai abinda na kasa ganewa ne a nan? Babu fa abinda a ka san Jonathan na aikatawa da kudin nan bayan biyan albashi. Kada a manta fa a wannan lokaci ne a ke sayar da kowacce gangar danyen mai a kan Dala 80. Bugu da kari, lokaci ne wanda a ka sace tiriliyan 2.6 a shekarar zabe, inda kuma mu ke ranto bashi domin mu biya albashi. Wadanne irin mutane ne wadannan haka? Shin keta ce ko sun tsani kasar ne ko kuma mu da ke zaune cikinta?

Karbar bashi ba laifi ba ne ga kasa. Muhimmin abu shi ne abinda ka yi da kudin da yadda ka tafiyar da shi. Na yi imani da cewa mu na da bukatar karbo bashi domin mu zamanantar da kayayyakinmu da su ka lalace a gaggauce. Za mu iya biyan bashin cikin sauki idan har za mu hana tafka almundahanar da a ke yi a halin yanzu cikin kasar tamu. Nijeriya ta na bukatar tashi tsaye wajen cigaban zamani, amma mu na bukatar akalla Dala biliyan 100 wajen zamanantar da ita. Dala biliyan 100 ba tare da aikata cin hanci da rashawa ba ya ishe mu. Duba fa ka gani, bashin da a ke bin mu na Dala biliyan 45 a yanzu ya bace a cikin sabunta abubuwanmu, ka kuma auna Dala biliyan 12 din da a ka ce Obasanjo ya batar a ‘samar da wutar lantarki’ ita ma ta yi batan dabo. Mu tuna irin ayyukan da za a samar da kuma yaye talauci da za a yi da kudin. Amma wasu mutane sun sace hatta kudin da za a biya albashi, sannan kuma su ka koma su ka karbo bashin Dala biliyan 45, domin sake biyan wannan albashin dai ta hanyar kudin tallafin mai na karya. Ba wai kawai ayyuka a kasa za a rasa saboda tafka rashawa ba, a’a, har mu da ’ya’yanmu ma an gadar ma na da bashin dala biliyan 45. Ba za mu iya cigaba da tafiyar da Nijeriya a haka ba.

Babu wata kasa a duniya wacce ta binkasa ba tare da yakar cin hanci da rashawa ba. Rashawa ta na kashe kasa ne; tuni ta ragargaza Nijeriya. A Malesiya da Singafur a na yin hukunci mai tsauri ne ga masu tafka rashawa. Idan kuwa haka ne ba abin mamaki ba ne don ’yar kankanuwar kasa kamar Singafur ta shiga sahun kasashe mafi cigaba a duniya. A lokaci guda kuma ginin Malaysian Petronas Twin Towers da ke Kuala Lumpur ya zama gini mafi tsororuwar tsawo a bayan kasa, wanda hakan ke alamta karfin tattalin arziki. Kada a manta, Malesiya ta na fitar da gangar danyen mai kasa da 600,000 ne kawai a kullum, yayin da mu kuma mu ke iya fitar da ganga miliyan 2.5 a rana guda. A hakikanin gaskiya ma dai, ba don almundahana ba, Nijeriya za ta iya fitar da ganga miliyan hudu a kullum. Ban da fa arzikin gas, wanda shi ma wani bangare ne mai zaman kansa a sha’anin danyen mai.

Jamus ce kasa mai karfin arziki a Turai, amma fa ta na cikin kasashen da a ke hukunta rashawa da tsaurin gaske. Kasar Sin, wacce ta zo daga bayan-baya ta zama ta biyu a duniya ta bangaren tattalin arzikin kasa, ta na cikin kalilan din kasashen da a ke zartar da hukuncin kisa a kan sace kudin al’umma. A Amurka, ba komai ba ne a sanyawa duk wani ‘mai ji da kansa’ ankwa a hannu, idan a ka same shi da laifin rashawa. Tambayi shugabannin Enron ko na Ponzi, Bernard Madoff ka sha labari. A yanzu haka da na ke yin wannan rubutu, wani babban janar a rundunar sojan Amurka, William Ward, a na kan tuhumar sa bisa aringizon kashe kudi.

Hakika mu san cewa, Jonathan ba ya damuwa kuma ba ya ji a jikinsa kan batun rashawa. Ya ce ba zai bayyana wa duniya abinda ya mallaka ba; ya kamata hakan ya sa mu fahimci yadda ya dauki batun rashawa.

Amma kasancewar Okonjo-Oweala a cikin gwamnati tabbas ba ya taimakawa kasar da komai. Ta na taimakon kanta ne kawai ta hanyar cigaba da kasancewa a cikin gwamnati. Har sai ta janye fassarar ma’anar da ta bai wa rashawa kumata fice daga cikin gwamnati, sannan ne ’yan Nijeriya za su fara kallon ta da sauran mutunci.

Wannan bayani Malam Sam Nda Isiah babban edita na Jaridar Lweadership ne ya rubuta a shafinsa na Monday Column.
Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment