Tuesday, September 11, 2012

Mallam Mudi Sipikin: Anya Najeriya Tayi Maka Halacci Kuwa?



Mallam Mudi Sipikin: Anya Najeriya Tayi Maka Halacci Kuwa?

Duk wanda ya san tarihin gwagwarmayar siyasa da akayi a najeriya ya san da cewa mudi sipikin yana daga sahun gaba na masu wannan fafutuka. Su mallam Mudi kusan su ne wadan da sukayi gwagwarmaya tun zamanin turawa, lokacin da Bature yake sawa a daukeshi aka yana karanta jarida, hakika wadan nan bayin Allah sunyi gwagwarmaya da turawa musamman ta nemawa Talakawan wannan kasa ‘yancin kai da ‘yancin walwala. Su mallam mudi sipikin sunyi gwagwarmaya tare da su Marigayi Mallam Aminu Kano Allah ya jikansa da irinsu mallam Lawan Dambazau da marigayi Sa’adu Zungur da sauransu.

Mallam Mudi sipikin yana daya daga cikin mutum 56 da akaje London comperence da su domin tattauna yadda za’a bada ‘yancin wannan kasa. Ta sanadiyar wannan taro na Landan Najeriya ta samu Mulkin kai daga hannun Turawan Burtaniya. A duk cikin wadan nan mutane da suka je wannan taro na Landan Mallam Mudi Spikin shi ne kadai mutumin da yake a raye yanzu haka. Amma haka aka yi bikin cikar Najriya shekaru hamsin da Samun mulkin kai, aka raba kyaututtuka ga Mutanan da suka nuna hazaka wajen dorewar wannan kasa, amma babu ko daya daga cikin ‘yan Siyasarmu da ya tuna da wannan bawan Allah, abin da zai iya zama abin kunya ga ‘yan siyasarmu musamman na Arewa. Bayan ita kanta gwamnati su kansu Talakawa basu kyautawa wannan dan tahaliki ba, domin duk gwagwarmayar da suka yi, ba sunyi ne dan kashin kansu ba, a’a sunyi ne domin amfanin Talakawa, andoke su an dauresu, duk dan saboda nemawa talakawa ‘yanci amma yanzu talakawa basa bukatar shawarwarin irinsu.

Duk wanda ya je Fagge gidan Mallam Mudi Spikin dole ya tausayawa wannan dan tahaliki dattijo mai halin dattako. Kaga gidan da yake a zaune, ba wani gida ne na kuzo mu gani ba, bayan kuma ga ‘yan siyasa can da basu tsinanawa kasar nan da komai ba, suna kwana a tafka tafkan Gidaje a Legas da Abuja da Kaduna. Bari mu kalli irin gwagwarmayar Siyasar da su Mudi Spikin suka yi tundaga kafa Jam’iyyar NEPU da sauran gwagwarmayar Siyasa.

Bari mu fara da tarihin kafuwar Jam’iyyar  NEPU,  kamar yadda tarihi ya bayyana an kafa NEPU ne a ranar 8-8-1950. Haka kuma, mutum takwas ne suka kafa ita wannan jamiyya wadanda suka hada da Bello Ijumu da Abba Maikwaru  da Mudi Sipikin, da Magaji danbatta da Baballiya Manaja  da Musa Kaula  da Abdulkadir danjaji  da kuma Garba Bida. Wadannan sune mutum takwas da suka kafa wannan jam’iyya gwagwarmayar ‘yanto talaka daga kangin bautar sarakuna da Turawa,  bari mu sake  komawa baya kadan domin mu kalli tarihi.
Asalain wannan guguwar sauyi ta fara ne tun lokacin da aka kafa jam’iyyar NCNC (National Council of Nigeria and the Camerroun) a ranar 26 ga watan Augusta a shekarar 1944.  Ita ce jam’iyyar siyasa  ta farko da za a iya kiranta ta kasa baki daya, domin kuwa ta watsu ko ina a Najeriya. Kuma itace jam’iyyar siyasa da ta fara kokarta wa wajen wayar da kan talakan Najeriya domin ya san ‘yancinsa da kuma kokarin samar musu da muryar gabatar da koke-koken da suke da su ga Turawan mulkin mallaka.
A zaben da jam’iyyar NCNC ta yi wa malam Sa’adu Zungur a cikin shekarar 1948 a matsayin sakatarenta na kasa da kuma kokarin da ta yi kokarin ganin cewa kowane bangare na kasar nan ya samu wakilci acikinta, wannan kuma wani gagarumin sauyi ne na siyasar kasar nan. Wannan wayon ‘yan mulkin mallaka ya mayar da hankali wajen jaddada bambance-bambance marasa masalaha da suke tsakanin ‘yan Kudu da ‘yan Arewa a siyasar Najeriya.
Bayan kafa NCNC acikin shekarar 1944 sai aka yi  yajin aiki na kasa baki daya, wanda kuma wannan yajin aiki shi ne na farko a tarihin  Najeriya wanda aka share  kwanaki 44 ana yi. Wannan yajin aiki bayan girgiza   tattalin arziki karkashin ‘yan mulkin mallaka da ‘yan barandansu wato sarakuna, ya kuma nuna afili inda mulkin mallaka yake da rauni da kuma nakasa.
Cif Makel  Imoudu dan majalisar gudanarwa na NCNC ne ya jagoranci wannan yajin aikin da ya gurgunta tattalin arzikin kasa  karkashin Turawan mulkin mallaka. A karkashin wannan fafutuka da NCNC ta yi ne aka dinga ganin jama’a a birane daban- daban suna shirya gangami da aka ringa Allawadai da Bature a fili balo-balo babu tsoro.
Bayan gama wannan gwagwarmaya ne kuma aka samu bullar Northern Elements Prograssibe Association wato NEPA a Kano wadda aka kafa a ranar 1 ga watan Disamba a shekarar 1946, wannan kusan ita ce jam’iyyar siyasar farko daga Arewacin Najeriya. Kafa wannan jam’iyya keda wuya ya bayyana cewa tsatstsauran ra’ayi shi ne mafarinta, wanda kuma shugabannin ta sune irinsu Habib Raji Abdalah da Abubakar Zukogi wadanda kuma alakarsu da Zik ba boyayya ba ce.
Ana cikin irin wannan hali ne kwatsam sai aka wayi gari da bullar sabuwar jam’iyyar Northern elements Prograssibe Union NEPU, kamar yadda muka fada a baya ita wannan jam’iyya ta kafu ne da mutum 8 kuma ranar 8 ga watan 8 a shekarar 1950.
Marigayi Alhaji Abba Maikwaru shi ne ya zama shugaban NEPU na farko  kuma Bello Ijoumu shi ne sakatare. Don haka NEPU ta fara ne amatsayin Jam’yyar siyasar Arewa mai sigar kishin kasa. Kasancewar NEPU ruhinta yana cikin talakawa da manoma da ma’aikata da sauran al’umma da ake dannewa kuma ake zalunta, don haka ne wannan jam’iyya ta sadaukar da manufofinta wajen gwagwarmaya domin ceto al’ummomi da aka danne da kuma kokarin tabbatar da ‘yancin dan Adam da dimokuradiyya.
A shekarar 1976 ne lokacin da aka samu zababbun shugabannin kananan hukumomi wanda aka raba su da sarautar gargajiya. Amma ba’a rabu da bukar ba  domin galibi ‘yan mulkin mallaka sun gadar da mulkin ne zuwa ga ‘yan barandansu na wannan lokaci wato ‘yan boko da sojoji marasa imani da kishin kasa, wadda a yanzu sun shirya komai sai su suke iya zama komai domin daga cikin shegantakar da suka fara yi shi ne cewa babu wanda zai iya tsayawa zabe a zabe shi sai mai takardar shedar gama makarantar sakandare wanda wannan lokaci kaso 90 duk talakawane da ba su yaki jahilci ba, ta hakane bayan mulkin mallakar Turawa kuma aka fuskanci mulkin mallaka karkashin bakake  wadanda su kadai ne ke iya zama gwamna ko ciyaman ko kansila, har ila yau kuma sun mai da karatun boko sai mai kudi ne zai iya yinsa, kuma sai tajirine zai iya biyan kudin shiga zabe.
Bayan wannan hali ne da ake ciki sai aka samu yakin basasar da ya kusan wargaza kasar nan wannan shi ne ya kawo cikas ga cimma nasarorin da NEPU ta sa a gaba ana cikin wannan hali ne sai aka samu bullar jam’iyyar ceton Al’umma wato PRP karkashin jagorancin Malam Aminu Kano wadda kuma aka kaddamar a ranar 28 ga watan Oktoba 1978, a Kaduna. Wannan ta baiwa malam  Aminu Kano damar gwagwarmayar ceto talakwa.
To ko me yabiyo bayan wannan gwagwarmaya? Kusan idan zamu amsa wannan tambayar sai mu ce babu abinda ya biyo bayan wannan gwagwarmaya face Butulci da cin-amana daga shugabanni Na siyasa wanda da gudunmawar talakawa mai yawa aka yi wannan wa-kaci-ka tashi.
Duk da kokarin da jam’iyyar Nepu da PRP suka yi na fitar da talaka daga halin talauci da kangin bauta, amma abin haushi da takaici shi ne haryanzu muna nan a gidan jiya. Talaka ya zama dan maula da tumasanci, baya kishin kansa sannan shugabanni basa kishin kasa, sun sace dukiyar kasa tare da Jahiltar da talakawa.
Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com
www.facebook.com/yasirramadan.gwale


1 comment:

  1. Tabbas na ji dadi da naga wannan rubutu kasancewa ta dalibi mai nazarin harshen Hausa,amma na kasa karanta shi yadda ya kamata saboda wani rubutun ya hade da hoton wasu litattafai da ke a wannan shafi naka.Dan Allah ka taimaka ka turo man wannan bayani a email di na.mustaphasalmanu00@gmail.com

    ReplyDelete