Thursday, September 13, 2012

Musulmi Allah Ya Bamu Hakuri



Musulmi Allah Ya Bamu Hakuri

Ya ‘yan Musulmi a cikin alkur’ani mai tsarki a sura ta 29 aya ta 2, Allah maigirma da daukaka yana cewa “shin tsammaninku dan kunyi Imani bazamu jarrabeku ba” hakika Allah ya jarrabi wadan da suka gaba cemu da tsanani da musiba da tashin hankali, har sai da sahabbai suka ringa tambayar Manzon Allah shin yaushe ne nasarar Allah zata zo? Manzon Allah ya ce ku sani Nasarar Allah a kusa take.

Ya ‘yan uwa wannan abin da ya faru ba sabo bane, sannan kuma ba abin mamaki bane. Idan zamu iya tunawa a shekarar 1988 wani marubuci dan Asalin kasar Indiya mazaunin kasar Burtaniya mai suna Ahmed Salman Rushdie ya taba rubuta wani littafi mai suna THE SATANIC VERSES wai shaidanun ayoyi a cikin al’qur’ani. Wannan littafi da wannan la’anannan mutum ya yi ya tayar da kura a daukacin kasashen Musulmi a wannan lokaci, inda da yawa daga cikin manyan malaman musulunci suka fitar da fatawar da take halasta jinin Salman Rushdie.

Wannan littafi karara karyata manzon Allah ne cin-fuska ne wa Musulmi baki daya. Amma saboda turawa makiya Allah ne makiya gaskiya wai ta dalilin wannan aka karrama Salman Rushdie da lamabar yabo mafi girma a duniya ta SIR, inda kuma aka bashi cikakkiyar kulawa a kasar Burtaniya, Allah ya la’anci Rushdie da ire irensa.

Daga cikin abubuwa na tashin hankali da suka samu Musulmi a wannan makon shi ne wayar gari da akayi da samun wani fim da yake nuna surar Manzon Allah Salallahu Alaihi wasallam, wanda wasu shedanu makiya Allah makiya zaman lafiya suka shirya, wanda kuma suka samu goyon baya daga muguwa annamimiya kasar Amerika. Ya Allah ka La’anci Dukkan masu cin-zarafin Musulunci da Musulmi. Haka nan tarihi ke maimaita kansa dangane da irin yadda wadan nan makiya Allah suke cin zarafin Musulunci.

Ya ‘yan uwa mu tuna Sahabin Manzon Allah mai daraja AMMAR BIN YASSIR. Shifa Ammar ba wai zagin manzon Allah akayi dan ya ji haushi ba, a’a kama shi aka yi aka ce shi da kansa ake son ya zagi manzon Allah! Ya ‘yan uwa shin akwai abinda ya kai wannan tashin hankali da firgici! Shin idan da kaine Ammar a wannan lokacin ya zaka ji a ranka? Haka nan Ammar ya aikata zuciyarsa tana cike da damuwa da bacin Rai da tashin hankali, ya zo ya Baiwa manzon Allah labara, manzon Allah ya tambayeshi shin ya kaji a Ranka? Ya shaidawa manzon Allah cewar yaji tashin hankali da damuwar da bait aba ji ba a rayuwarsa.

Shakkak babu wannan abinda ya faru abin bakin ciki ne da damuwa da tashin hankali. Ya ‘yan uwa wannan ba zai zama sanadiyar da zamu afkawa mutunan da basu jiba basu gani ba, mu sani cewa Allah ya riga ya bamu hakuri, Manzon Allah ma ya bamu hakuri. Mu nuna fushi da damuwarmu ta hanyoyin da suka dace da shari’ah.
Allah ya huci zuciyarmu

Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com
www.facebook.com/yasirramadan.gwale

No comments:

Post a Comment