Sunday, November 29, 2015

Zancen Zuci . . . 2015


ZANCEN ZUCI . . . 2015

BEFORE:

* Ai yana hawa komai zai canza . . .

* Shi kad'ai ne zai iya Gyara kasarnan!

* Shi ne kad'ai mai gaskiya!

* Shi ne mutumin da ya san maganin matsalolin kasarnan.

* Idan ba shi ba waye zai iya gyara Nijeriya?

* Daga ranar da aka rantsar da shi Nijeriya zata hau saiti.

* . . . Ai yana hawa duk matsaloli sun kare.

* Matsalar Boko Haram ta zo karshe, yana hawa.

* 'yan matan Chibok, ai kamar an sako su, an gama...

* Kayan abinci da na masarufi duk zasu yi arha...

* Duk barayin kasar nan sai ya kamo su...

* Su Ngozi da su Diezani sai sun dawo da abinda suka sata!

* Man fetur zai yi arha, yana hawa zai dawo N40.

* Zai daidaita farashin Nera da Dala.

* Ku dai kawai ku zabi canji.

* (waka) Sai Baba Buhari . . . Sai mun yiwa . . . Zigidir

AFTER:

* Bari kuga ya fara nad'e nad'e.

* Yanzu wad'annan Ministocin har sai an b'ata wannan lokacin dan zabosu, kayya!?

* Haba! Nijeriyar da aka rusa a shekaru 16... sai adduah

* . . . ta yiwa Nijeriya illa ba karama ba!

* A dai yi hakuri, komai a sannu ake binsa.

* Baba ka cika tafiyar hawainiya (Baba Go-Slow).

* Ai fa sai munyi hakuri gyaran Nijeriya sai a hankali.

* ... Wallai mutane sun cika gajen hakuri!

* Daga hawansa har mutane sun fara korafi?

*Bam nan bam can... anya canji ko sanji?

* Watansa shida fa, Haba!

* Ai dan ba shi yayi bajat din bane.

* Ku jira zuwa Janware ku gani idan anyi bajat.

NOW:

* Wannan wane irin Canji ne?

* Babu Manfetur gashi yayi tsada ga masifar layi.

* (waka) Baba Buhari yaci zabe, Abinci yayi tsada...

* Wai Gwamnanoni ba zasu iya biyan albashi ba?

* An kai hari kasuwar Farm Centre a Kano, Kaiyya!

* Baba ya cika yawo fa...

* Wai Iran zashi?

* Sarkin yawo yau kuma an tafi Malta da Faransa.

* Har fa yanzu Bamabami basu dena tashi ba fa!

* Anya kuwa Buharin nan...?

* A ce komai yayi tsada haka?

* Tab! Farashin Dalar Amurka fa ya kai 242.

* Rayuwa fa tayiwa masu karamin karfi tsanani...!

*Bla bla bla

Wad'nnan su ne wasu daga cikin irin kalaman da naji mutane da yawa na fad'a,  kafin da bayan zab'e da kuma yanzu. Har ya zuwa yanzu mutane na cigaba da bayyana ra'ayinsu akan salon tafiyar Gwamnatin Baba Buhari.

Yasir Ramadan Gwale
29-11-2015

No comments:

Post a Comment