Saturday, November 14, 2015

SUWA ZA A ZARGA DA KAI HARIN BIRNIN PARIS NA FARANSA?



SUWA ZA A ZARGA DA KAI HARIN BIRNIN PARIS NA FARANSA? 

A tsakar daren jiya wayewar garin yau Asabar kafafen yada labarai na kasar Faransa suka bayar da labarin wasu hare hare da aka kai birnin Paris shalkwatar Gwamnatin kasar Faransa, inda mutane fiye da 100 rahotanni suka nuna cewar sun mutu. Bayanai sun tabbatar da cewar gurare biyar aka nufa da wannan hari,  inda hare hare ya rutsa da su sun hada da:

1- Harin Bom a Harabar wani filin wasa mai suna Stade De France, inda aka ce Shugaban kasar Faransa, Farnciou Hollande yana wajen inda yake kallon kwallo tsakanin Faransa da kasar Jamus. Bayanai sunce a gigice a aka fice da Shugaban kasar daga filin wasan, inda hankalin mutane ya tashi, kowa ke gudun yada-kanin-wani.

2- Anyi Garkuwa da mutane kusan 100 dari a wani gidan disco da ake kira Bataclan concert hall, inda daga bisa ni aka ce an kashe gaba dayan mutanan da ke cikin gidan disco din.

3- Waje na uku da aka kai wannan hari shi ne wani katafaren gidan cin abinci da ake kira  Le Carillon, inda aka dinga harbin kan-me-uwa-da-wabi. Rahotanni sun ce kimanin mutane 11 suka hallaka a yayin wannan bude wutar.

4 - Waje na hudu da aka kai wannan hari ita ce wata karamar mashaya da ake kira LA Belle Equipe inda aka budewa mashaya wuta bayan sunyi mankas, bayanai sunce ba a samu asarar rayuwaka da yawa a mashaya ba, amma dai an samu jikkata da yawa.

5- Waje na biyar kuma na karshe da aka kai wannan hari shi ne wani gidan cin abinci da ke sayar da kayan kwalama da ake kira Le Petit Cambodge, anan ma maharan sun bude wuta kan masu ciye ciye da lashe lashe babu ji babu gani.

A Jumlace bayanai sun ce an kashe mutane sama da 120 a daren jiya a Birnin Paris. Wannan harin yayi matukar girgiza  Faranasawa ma zauna birnin Paris, tuni bayanai suka ce Shugaban kasar Hollande ya soke halartar taron kasashe masu karfin Tattalin arziki da ake kira G-20 da zai fara gudana yau Asabar a kasar Turkiyya. 

Idan ba a manta ba, Jaridar nan ta Charlie Hebdo mai zanen hotunan batanci, tayi wani zanen batanci akan wani jirgin kasar Russia da yayi hatsari a Birnin Sinai na kasar Masar ya kashe duk mutanen da ke cikinsa, zanen dai ance yayi matukar bakantawa Gwamnatin Kasar Russia rai, inda aka ce Shugaban kasar VV Putin ya nuna rashin jin dadinsa kan wannan cin mutunci da Charlie Hebdo ta yiwa kasar, ba tare da girmama rayukan wadan da suka rasu ba.

Tuni dai kasashen duniya ciki har da kasar ta Russia suka taya Faransa jimamin ab inda ya faru. A ganina wannan harin ba shida wata alaka da Musulunci balle a dora laifin ga Musulunci. Amma dai al'adar kasashen Turai ce na dora laifin irin wannan hari akan kungiyoyin 'yan tayar da kayar baya da ke jingina kansu da Musulunci, tun ba a kai ga yin binciken gano hakikanin su waye suka kai harin ba. Allah masani.

Yasir Ramadan Gwale 
14-11-2015

No comments:

Post a Comment