Wednesday, November 18, 2015

Sa'udiyya: Babu Wanda Yafi Karfin Doka Hatta Sarki Salman


SA'UDIYYA: BABU WANDA YAFI KARFIN DOKA HATTA SARKI SALMAN 

Gidan Talabajin na Al-Arabiyya ya ruwaito Sarkin Sa'udiyya Salman Bin Abdulaziz yana shaidawa manyan jami'an Gwamnatinsa cewar kaf fadin Kasar Sa'udiyya babu wanda yafi karfin doka hatta shi kansa (Sarki Salman) bai fi karfin doka ba. Sarkin ya kara da cewar duk wani dan kasar ta Sa'udiyya na da 'yanci ya kalubalanci kowa a Kotu matukar anci zarafin sa ko an take masa Hakki ko da shi da kansa ne za a iya gurfanar da shi a kotu.

Sarkin ya fadi haka ne, a ranar Laraba a yayin da yake gabatar da jawabi ga manyan jami'an Gwamnati dake Yaki da cin hanci da rashawa. Sarki Salman ya shaidawa al'ummar Sa'udiyya cewar kofar sa da kunnen sa a Bude suke dan sauraron korafin duk wanda aka takawa Hakki, yace za a biyawa kowa hakki ba tare da nuna bambanci tsakanin dan Sarauta da wanda ba shi ba. Sarkin yace, yafi damuwa da hakkin al'ummar kasar sama da hakkin sa a matsayinsa na Salman Bin Abdulaziz. 

Haka kuma, Sarkin ya gargadi jami'an hukumar Yaki da cin hanci da karbar rashawa cewar su sani Allah da ManzonSa sune suka fara Yaki da cin hanci da rashawa, dan haka su yi aiki da gaskiya da amana. Jama'a  Wannan fa shi ne, Sarkin Sa'udiyya Salmanu Dan Abdulaziz wanda Iran da Shiah da 'yan kanzaginsu a Nigeria  kullum suke yiwa jafa'i da fatan masifa da bala'i su auka musu, kullum bakin cikinsu Alsaud. Ya Allah ka yiwa bawanka Sarki Salman jagoranci, Allah ka taimake shi ka kunyata makiyansa na sarari da na b'oye. Allah ka taimaki adalan Shugabanni a duk inda suke, Allah ka taimaki kasarmu Nigeria. 

Yasir Ramadan Gwale 
19-11-2015

No comments:

Post a Comment