Wednesday, September 30, 2015

Kiyayyarsu Ga Saudiyya


KIYAYYAR SU GA SAUDIYYA

Bama shakkar kasancewar wasu daga cikin Larabawa masu matukar nuna bambanci da wariyar launin fata. yanayin launinmu bakake, da farare wata hikima ce ta Allah. Amma mafiya yawan masu zagin Sa'udiyya ba suna yi bane, domin nuna kyama ga bambanci launin fata, illa suna nuna matukar kiyayyarsu gareta ne sabida kasancewarta, Daula ta SUNNAH da suka tsaya tsayin daka wajen yada tauhidi da kadaita Allah da Bauta.

Wannan wani mugun ciwo ne, da ya tsayawa Iran a makoshi, shi ysa kullum burinsu kambama duk wani abu na kuskuren mamlaka, domin jefa kiyayyarta a zukatan usulmi wadan da Ba larabawa, wanda hakan yana bayuwa ne zuwa ga kiyayyar Addini. Suna mugun kin Sa'udiyya basa sonta, sabida abinda suke kira WAHABIANICI.

Mu kuma muka ce munji mun gani, mu din Wahabiyawa ne, cikin makiya ya kumbura ya fashe. Da damansu wallahi ba zasu iya bayyana cewar su SHIAH suke yi ba, sabida sun san karya ce, bata ce, kuma ba addini ba. Shi yasa a koda yaushe suke fakewa da kankanan abubuwa domin bayyana kiyayyarsu a fili.

Ba zaka sha mamaki, sai ka taba Iran nan zaka ga martani ta ko ina. Mu kuma mun san karya ne, Iran Jamhuriyya ce ta Shedanu da shedanci babu wani Alkhairi ko kadan a tare da su, banda farirci da kafurci da nesanta mutane ga barin Addini. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, bai gushe ba yana adduar Allah ka fishshemu dariyar makiya. Allah ka maida musu kaidinsu garesu.

Yasir Ramadan Gwale
30-09-2015

No comments:

Post a Comment