Monday, September 7, 2015

Asirin 'Yan Shiah Ya Tonu


ASIRIN 'YAN SHIA'AH YA TONU

A makon da ya gabata ne, Shugaban hadaddiyar kungiyar Izala ta kasa Sheikh Abdullahi Bala Lau ya jagoranci tawagar kungiyar Malaman Musulunci ta Africa, inda suka kaiwa sabon Shugaban kasa Muhammadu Buhari ziyara a fadar Gwamnati. Bayan wannan ziyara ne hotunan wannan ziyara suka bayyana a kafafen sadarwa inda aka ga Shugaban kasa tare da Malaman Musulunci Africa. A hoton akwai manyan Malaman Sunnah na Nigeria da suka hada Sheikh Bala Lau da Imamu Ahlussunnah Wal Jama'ah Sheikh Abdulwahab Abdallah da Sheikh Dr. Muhd Sani Umar Rijiyar Lemo da Sheikh Alhassan Said Jos da Sheikh Hassan Yakub Katsina da sauran Malamai daga kasashen Africa da suka kai wannan ziyara.

Ashe wannan ziyara bata yiwa Mabiya Addinin Shiah na Najeriya dadi ba. Inda suka bi wannan ziyara da mugun sharri da hakan ya kwaye musu zani tare da tsiraita shi'ah  bainar jama'ah. Jaridar AlMizan ta 'yan Shiah, ta Juma'ar makon jiya, ta buga hoton waccan ziyara tare da yi masa taken, "Israeli Na Zawarcin Shugaban kasa Buhari". 'Yan Shiah da yake miyagu ne makaryata, sun saba shararata,  sai suke kokarin canjawa abin suna da nufin nunawa mabiyansu cewar Malaman Sunnah da suka kai wannan ziyara, tare da daurin gindin kasar Israeli suka je. Kaga wannan tsabar karya ne da sharri da jafa'i.

Da yake su 'Yan Shiah mugayen Jahilai ne. Sun jahilci meye Gwamnati da yadda ake mu'amala tsakanin Gwamnati da Gwamnati. Sun manta cewar kasar Israeli na da Jakada a Najeriya kuma itama Najeriya nada nata jakadan a Isaeli wanda duk wata huldar Diplomasiyya tsakanin kasa da kasa ana yinta ne tsakanin wadannan bangarori guda biyu dake Abuja da Tel Aviv. To, amma su Shaih da yake sun jahilci wannan sai suke kokarin nunawa mabiyansu cewar Malaman nan ai Israeli suke yiwa aiki, kuma ita ta sanya su.

Shin yanzu dan Allah su ba zasu ji kunyar bayyana hakan ba? Bahaushe yace idan mai fadar magana wawa ne to daga masu sauraro akwai wadan da ba wawaye bane. Dan haka, anan Allah ya tonawa Shiah asiri. Shugaban kasa Muhammadu Buhari da aka kaiwa waccan ziyara, zai fahimci mugun sharri na mabiya Shiah gareshi da kuma al'ummar Najeriya. Domin yasan cewar ziyarar da aka kai masa ba tada wata alaka ko ta kusa ko ta nesa da Israeli. Haka kuma, duniya na kara fahimtar irin mugun kulli da mummunan fata da Shiah suke yiwa Najeriya.

Dan haka, anan ya dace al'umma su fahimta cewar Shiawa ba mutanan Alkhairi bane, kullum fatansu sharri da makida ga al'ummar Muslmi. Sam basa fatan ganin al'ummar Musulmi sun hada kai waje guda dan yiwa addinin Allah aiki. Ko da yaushe fatansu, shi ne sharri da rarrabuwa tsakanin Musulmi. Muna fatan Allah ya dafawa ayyukan waccan kungiya ta Malman Africa. Allah ka shiga cikin al'amarinta.  Allah ka taimaki Musulunci da Musulmi, ka rusa Shiah da mabiyanta da shugabanninta. Allah ka taimaki duk masu taimakon addininka.

Yasir Ramadan Gwale
07-09-2015

No comments:

Post a Comment