Sunday, September 6, 2015

Allah Ya Kara Daukaka Malam Nuhu Ribadu


ALLAH YA KARA DAUKAKA MALAM NUHU RIBADU 

Jiya Asabar fitacciyar Jarida a Nigeria THISDAY tayi bikin karrama wasu fitattun mutane a Nigeria a saboda irin kwazonsu da san cigaban kasa da suka nuna. Malam Nuhu Ribadu na daya daga cikin mutanan da wannan jarida ta karrama da Award mai suna "Game Changer", a sabida irin kwazo da jajircewarsa da ya nuna wajen ganin an Yaki cin hanci da Rashawa a Najeriya. Ba shakka, karrama fitattun mutane da suka nuna kwazo da gaskiya a aikin su abu ne da ya dace. Malam Nuhu Ribadu mutum ne mai gaskiya da tsoron Allah, wanda ya samu wannan shaida a dukkan sassan Najeriya. Ina amfani da wannan damar wajen taya shi murnar samun wannan kyakkyawar Shaida.

 2019 RIBADU MUKE FATA! 

Yasir Ramadan Gwale
06-09-2019

No comments:

Post a Comment