Sunday, November 23, 2014

Zancen Zuci


Har kullum tambayar da take raina ita ce, Shin yanzu idan aka samu 'yan ta'adda da suka labe cikin al'umma a London da Warshington da Tel Aviv shin wadannan kasashen zasu bada Umarnin a yi amfani da jirgi mara matuki yayi ruwan bamabamai daga sama a rurrusa makarantu da asibitoci da kantuna da gidajen jama'a sauransu duk da sunan yakar 'yan ta'adda? Mu kalli yadda Netanyahu ya ragargaza Ghazza da sunan yakar 'Yan Hamas; Ga kuma yadda ake rushe gidajen jama'a a Iraqi da Suriya duk da sunan yakar ISIS. An hada karya da gaskiya ta hanyar amfani Khawarij sun sani ko basu sani ba ana cutar da Musulunci da Musulmai.

Wadannan fituntunu ba zasu taba karewa ba sai dai ma sabbi su sake bullowa. Domin Manzon Allah yayi ishara da faruwar kashe kashe a karshen duniya da bayyana tsiraici da aikata alfasha a bainar jama'a da fashi da sata da kwace. Babu wani abu da baya faruwa a yanzu duk wani nau'i na aikin sabo ana yinsa a cikin al'ummar Musulmi. Mace ta kashe mijinta, Miji ya kashe matarsa; d'a ya kashe iyayansa, uba yayi zina da matar dansa, uwa tayi zina da mijin 'yarta. Dan Adam yayi zina da dabba, ayi zina tsakanin mace da mace, namiji da namiji. Duk wannan ba sai anje da nisa ba laifuka ne da sukai katutu a tsakanin al'ummarmu.

Wasu sukan dauka cewa Wai Musulmi ba zai iya kashe Musulmi ba. Duk wanda suke da wannan tunani yana da kyau su je su karancin tarihin Khawarij. Wanda ya kashe Sayyaduna Usman RA Musulmi ne, haka wadan da suka kashe Aliyu dan Abi Talib da Dalha da Zubair duk masu ikirarin Musulunci sukai wannan aika aika.


'Yan shiah masu kiran kansu Musulmi suka fille kan jikan Manzon Allah SAW. Ya dan uwa ka kyautata tsakaninka da Allah, kaji tsoran Allah a cikin lamuranka, ka bautawa Allah gwargwadan ikonka, kar kaci hakkin wani, kar kayi shirka In Sha Allah zaka samu mahaliccinka mai tsanani Rahama ne da Jin Kai. Allah ka yafe mana laifukanmu wadan da muka sani da wadan da bamu sani ba.

Yasir Ramadan Gwale
19-11-2014

No comments:

Post a Comment