Thursday, November 13, 2014

Sheikh Ahmad Abubakar Gumi

Sheikh Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi: Akramakalahu yanzu na fara Nazarin Nasihar ka.

Ba shakka Dan danon magani ba shida dadi ko kadan a wajen mara lafiya da ake kokarin ceto rayuwarsa, amma tabbas shi ne abinda yafi bukata. Sau da dama mara lafiya har danne shi ake yi a dura masa magani, amma yana shure-shure yana kukan kura yana nuna baya so, amma haka nan ake dura masa maganin yana baya so, baya so. Karshe kuma maganin da ya dinga fatali da shi a baya sai ya zama silar samun warakarsa. Ai ko likata ma yasan Allah ka bada lafiya ba garin magani ba. Amma kuma haka sunnar Allah take, idan anyi rashin l;afiya aka sha magani sai kaga an samu sauki garas. Dan haka magani komai dacinsa a danne mara lafiya a bashi ya sha ko yana so ko baya so, a gaba shi zai fi kowa murna da maganin da aka bashi.

SAI DAI KUMA: Shi fa magani yana da lokuta kayyadaddu kuma kididdigaggu, idan akai sa'a aka sha akan lokaci, cikin dace sai a samu waraka. Kai akwai yana yin da idan ma aka baiwa mara lafiya magani tamkar kara masa ciwo ake yi. Dan haka kiyaye ka'idar shan magani ita kanta na taimakawa mara lafiya. Haka nan shima mai bada magani.

HAKA KUMA, wasu suna ganin ita gaskiya dandanonta yayi kama da na magani mai daci. To dan haka idan har mun gamsu cewa ita gaskiya daci gareta, to meye na tada jijiyar wuya? Allah ya baiwa mara-laiya lafiya, ya karawa mai lafiya lafiya.

Yasir Ramadan Gwale
13-11-2014

No comments:

Post a Comment