Friday, November 28, 2014

Kwankwaso Ya Shammacemu

KWANKWASO YA SHAMMACE MU

Yanzu dai dukkan kwannafi ya kwanta dangane da wanda Gwamna Kwankwaso zai zaba wanda zai yi takarar Gwamna a APC. Wannan dai zabi ne na mai girma Gwamna ba zaben fidda Gwani bane, kamar yadda aka ce a zaben da ya gabata Malam Ibrahim Shekarau ya zabi Malam Salihu Sagir Takai ba tare da anyi zabe ba. Daman ance Tarihi hakanan yake maimaita Kansa.

Sai dai wannan zabe da akaiwa Ganduje ba shakka ya shammaceni, dan banyi tsammanin haka. Amma kuma nayi Imani da Allah cewa Malam Umar Abdullahi Ganduje mutumin kirki ne mai kamala da sanin yakamata.

Duk a cikin masu neman takara a APC alal hakika nafi samun nutsuwa da Ganduje dan na san ba zai cuci al'ummah ba. Ina taya shi murnar wannan zabi da akai masa.

Ina kuma adduah tare da rokon Allah ya sa ya zamar mana karkatacciyar kuka mai dadin hawa a zabe, Malam Salihu Sagir Takai ya kada shi cikin sauki. Ina da kwarin guiwar cewa Dan Takararmu Malam Salihu Sagir Takai zai baiwa Ganduje ruwa a wannan zabe mai zuwa da tazara mai yawa.

Na kuma tabbatar cewa Malam Salihu Sagit Takai yafi Ganduje cancantar zama Gwamnan Kano a zaben 2015. Ina kuma da yakinin cewar zamu shammaci Kwankwaso a wannan zabe. KANO TAKAI MUKE FATA. ALLAH YA AMINCE MAKA MALAM SALIHU TAKAI.

Yasir Ramadan Gwale
28-11-2014

No comments:

Post a Comment