Wednesday, October 3, 2012

ZABEN AMERIKA: Abinda Mutane Da yawa basu Fahimta Ba!



ZABEN AMERIKA: Abinda Mutane Da Yawa Basu Fahimta Ba!

Yanzu a wannan karni na ashirin da daya (21) kasar Amerika it ace kasar da take jagorantar tsarin jari hujja a duniya. Amerika it ace kasar da kusan tafi kowace kasa karfin tattalain arziki, da kuma, karfin makamashi, wanda yanzu kusan shi ne yake juya wainar siyasar duniya. Wato tsarin siyasa da karfin tattalin arziki, a wannan karnin baka samun karfin tattalin arziki sai ka mallaki karfin makamashi kamar yadda Henry Kissinger ya fada a hirar da ya yi da jaridar Daily Squab a ranar 27 ga watan Nuwamban 2011, inda yake cewa “wanda yake da iko akan makamshi, to ya sami iko akan kasashe” wannan iko da kasar Amerika take da shi kusan shi ne ya bata ikon juya kasashen duniya yadda taga dama.

Siyasar kasar Amerika ta sha bamban da siyasar sauran kasashen duniya musamman kasashen masu tasowa. Siyasar kasar Amerika tana cike da sarkakiya da kutunguila da makirci na kin karawa, sannan uwa uba kuma abinda yake jan linzamin siyasar kasar Amerika shine ‘tattalin arziki’. Wato baka iya zama mai fada aji sai kana da karfin tattalin arziki kamar yadda da yawa suke da masaniyar cewar kasar Amerika kusan it ace ke kan gaba wajen jagorancin kasashen duniya mafiya karfin tattalin arziki da ake kira da suna G20 da kuma kasashen masu karfin arzikin masana’antu na G8 dama ko ‘G’ wacece, duk zaka samu Amerika it ace take da karfin fada a ji a tsakanin Dukkan kasashen da suka kulla kawance.

Kusan tun bayan faduwar kakkarfar tarayyar Soviet wadda Rasha ta yiwa jagoranci Amerika ta samu damar cin karanta babu babbaka wajen yin yadda taga dama da kasashen duniya a mastayin jagorarsu. Duka da rusashshiyar tarayyar Sobiya karkashin jagorancin Rasha da kasar Amurka ba wani abu suke yiwa ba, illa irin dumbin arzikin makamshi da Allah ya huwacewa wannan duniyar, sai dai sun dan sha bamban ta wata fuska, domin ita kasar Rasha tafi mayar da hankalinta ne akan abinda ya shafi makamashin iskar Gaz, wanda nasan da yawa jama’a suna sane da katafaren kamfanin isakar gas dinnan na kasar Rasha da ake kira Gazprom. Dalilin da ya sanya kasar Rasha tafi mayar da hankali akan abinda ya shafi makamshin isakar gaz yana da alaka da yanayinsu na dusar kankara a Rasha da kuma gabashin Turai, wanda wannan kamfani na Gazprom kusan shine babban kamfani mallakar Rasha da yake samar da makamashin isakar gas ga ita kasar rashan da kuma kasashen da ke gabashin Turai harma da na yammacin turai; sanna kuma ita a nata bangaren kasar Amerika tafi mayar da hankali ne akan abinda ya shafi gurbataccan man fetur da dangoginsa, saboda manayn masana’antun da take da shi.

Dan haka siyasar kasar Amerika kusan tana tafiya ne kacokaan akan abinda ya shafi cigaba da mamayar tattalin arzikin kasashen duniya. Ina jin jama’a bazasu manta da kamfanin kasar Amerika mai suna Halliburton ba, wanda aka zarga da badakar cin hanci ta dubban miliyoyin daloli akwanakin baya a Najeriya, shi wannan kamfani mallakar wasu manyan attajiran kasar Amerika ne wandanda kuma sune suke juya akalar siyasar kasar Amerika, shi wannan kamfani wanda cibiyarsa take a Texas, Iyalan Bush da Iyalan Bin Laden suna da hannun jari mai girma acikinsa. A kashin gaskiya siyasar Amerika kusan tafi ta kowace kasa makirci da mafiyanci da kutunguila da kuma sarkakiya, sanannen abu ne cewar akwai alaka mai karfi tsakanin manyan kamfanonin jari hujja na Amerika da ake kira Corporate Capitalism da gwamnatin Amerika, domin wadannan gungu na mafiyawa sune suka shigar da duk wani shugaban kasar Amerika fadar white House da kuma wakilan majalisar dokoki da ta dattabai, dan haka sune suke samar da shugabannin Amerika da wakilai wadan da zasu kare manufofinsu na kasuwanci.

Tsohon shugaban kasar Amerika Franklin D Roosevelt  ya taba fada a gaban majalisar dokokin Amerika a ranar 29 ga watan Afrilun shekarar 1938 cewa “cin gashin kai na tsarin demokaradiyya ba zai taba zama cikin aminci ba, idan har akwai wasu tsirarun mutane da suka kafa wasu cibiyoyi da karfinsu ya fi na gwamnatin demokaradiyyar da jama’a suka zaba. Wannan yana nufin cewa gwamnati ta zama ta wasu dai-dai kun mutane da wasu cibiyoyi da zasu ringa sarrafa ta daga nesa kenan”. A hakikanin gaskiya wannan shine abinda yake faruwa dangane da siyasar kasar Amerika, duk ihun da wani shugaban kasar yake yi ko daga Democrat yake ko daga Republican yana yi ne karkashin kulawar wadannan shaidanun mafiyoyi.

Wani muhimmin misali akan haka shine, daya daga cikin manyan kamfanonin mai na kasar Amerika mai suna UNOCAL ya taba nuna maitarsa a bainar jama’a dangane da dumbin albarkatun makamashin da suke kwance a tafkin Caspian sea, daya daga cikin manyan shugaban kamfanin mai kula da alaka tsakanin kasa da kasa Mista John J Merosca ya taba gabatarwa da kwamatin dake kula da alaka tsakanin kasashen na majalisar dokokin Amerika a ranar 12 ga watan fabrairu na shekarar 1998 cewa “ akwai dumbin albarkatun makamashi da Allah ya huwacewa yankin tekun Caspian”  daga nanne kuma ya yi wata ishara mai cike da kitumurura waddaa zata kai ga shimfida bututan da zasu kai ga hako wadannan albarkatu da ke kwance a wannan tafki.

Yana da kyau mu fahimta cewa babu wani bambanci na kuzo mugani dangane da siyasar cikin gida da waje tsakanin manyan jam’iyyun kasar Amerika guda biyu wato Democrat da Republican. Kasar Amerika kusan sha-kundum ce, siyasar kasar Amerika ta wuce ayi kamfe da suna wutar lantarki ko ruwan famfo ko harkar lafiya ko harkar ilimi, fiye da shekaru dari kasar Amerika ta fitar da kanta daga wannan mastalar, dan haka wadannan sunyi kadan su mamaye siyasar kasar Amerika.

Bugu da kari, ga duk wanda yake bibiyar yakin neman zaben da ake yi tsakanin Barack Obama da Mitt Romney kusan batu ne guda uku da suke jayayya akansa! Abu na farko shi ne, Shin kasar Rasha abokiyar gabar Amerika ce ko kuwa kawarta ce da akewa juna kallon hadarin kaji, sannan kuma da batun Shin akaiwa Iran hari a yanzu ko kuwa sai wani lokaci na nan gaba, duk kuwa da cewa shi kansa wannan batu na kasar Iran wani batu ne mai cike da sarkakiyar gaske, haka kuma, da batun shin Amerika zata jibge dakarunta a kasar Syria ko kuwa. Wanda wannan batu na Syria yake kara nuna cewa ba mai karewa da wuri bane domin shima yana cike da makirci da kutunguila irin ta shaidanun ifuritan Amerika masu juya tsarin jari hujja, sannan da ibilisan kasashen irinsu Rasha da chana da Iran. Kada ka dada kada ka raga wadannan sune manyan batutuwan da suka mamaye yakin neman zabe tsakanin Obama da Romney.

Abinda zai kara tabbatar da cewar duka wadannan jami’iyyu na Amerika bakisnsu daya, inda suka saba shine wajen aiwatarwa, misali jami’iyyar Democrat ta Bill Clinton ta shiga kasar Afghanistan ta hanayr tattaunawar Diplomasiyya, yayin da jam’iyyar Republican ta George Bush ta shiga Afghanisatan ta hanayr amfani da karfin soji, idan akwai bambanci to wannan shine bambancin dake tsakanin wadannan jam’iyyu amma duk manufarsu day ace, kawai a aiwatarwa suka bambanta. Shugaban Obama ya taba fada cewa gwamnatin kasar Amurka kamar wani jirgin kasa ne da ya yake tafiya duk shugaban kasar Amerika sai dai ko ya kara gudunsa ko kuma ya rage gudunsa, amma ba zai iya tsaida shi ba, ballantana kuma ya canza masa akala daga yamma zuwa gabas, wannan shine kusan hakikanin makirci da kutunguilar siyasar Amerika.

Haka kuma, shata iyakokin manufar kasar Amerika dangane da kasashen duniya aiki ne na kwararrun cibiyoyi, ba na jam’iyyar siyasa ba. Wato wannan yake kara tabbatar mana da cewa su wadancan shaidanu karkashin Corporate capitalism sune suke yin uwa suyi makarbiya a harkar siyasar kasar Amerika bayan anyi zabe an gama. Wannan yake nuna Amerika ba kamar kasashene masu tasowa ba, ta yadda duk shugaban da yazo yana iya rusa Dukkan ayyukan da magabacinsa ya yi, sannan ya dora nasa sabo, Amerika tasha gaban haka, duk kwarewarka da wayo da dabara dole ka tafi akan wannan tsari da kazo ka tarar.
Dan haka duk wasu ihu da hayaniya da jam’iyyun Democrat da Republican zasu yi, bai wuce share hanyar da za’a cimma wadannan manufofi na kasarba.

Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com
www.facebook.com/yasirramadan.gwale

No comments:

Post a Comment