Sunday, November 27, 2011

Rikicin Kabilanci da na Addini a Najeriya: Ina Mafita

Najeriya kasace da ta fi kowacce kasa yawan jama'a a nahiyar Afrika kuma kasace mai kabilu daban daban ga kuma yaruka masu yawan gaske kusan kididdiga ta nuna akwai yaruka sama da 250 a Najeriya, kamu Allah ya albarkaci Najeriya da Dumbin arzikin da kusan baitaba baiwa wata kasa aduniya ba kamar yadda masana suke fada, Haka kuma najeriya tana da addinin musulunci da kirista da kuma masu addinin gargajiya.

Duk dan Najeriya ba zabinsa bane ya kasance dan asalin wannan kasar, haka Allah yaso ya hada kura da akuya agarke daya haka Allah ya liccemu kuma ya hadamu a wannan guri da ake kira Najeriya bada zabin mu ba, kuma yayimu kabilu daban daban, wani Bahaushe wani Inyamuri wani kuma bayerabe haka kuma wani dogo wani gajere wani baki wani fari wani mummuna wani kuwa idan ka ganshi kamar shi yayi kansa, Allah mai yadda yaso, hakadai Allah ya yimu bisa zabinsa kusan da za'a tambayi dan Najeriya me ye zabinsa watakila da ba nan zaice ba. mukam muna yiwa Allah godiya da muka kasance 'yan Najeriya kuma masu kishin kasarsu kamar yadda kowanne mahaluki aduniya yake kishin kasarsa, misali duk dan kasar Mesedoniya baiyarda da cewa wata kasa tafi kasar sa ba, domin kuwa tun a makaranta duk yaro ana gaya masa daga Allah sai mesedoniya don haka ne suke alfahari da kasarsu da kuma yarensu.

Yawaitar rikicin Addini dana kabilanci a najeriya, mu duba rikicin kafancan a jihar kaduna wanda akayi ashekarar 1987, mutum nawa ne suka rasa rayukansu da dukiyoyinsu basuji basu gani ba, aka maida wasu marayu wasu mata kuwa suka koma zawarawa.

Sannan mutum nawane wadan da aka hallaka sunaji suna gani saboda kabilanci a Idiyaraba a shekarar 2002, Haka kuma mutum nawa aka kona aka lalata musu dukiyoyinsu aka raba iyaye da 'ya 'yansu a shagamu ashekarar 2001 badon komai ba sai kawai don kabilanci shin su sukayi kansu ne? Mu kalli yadda matasa dauke da makamai suka dirarwa kauyen agbohol a jihar bunuwai ashekarar 2004 wai suna ikirarin su mutanen ba 'yan asalin kauyen bane kawai sabida bambamcin kabila.

An kashe mutane da yawa kana kuma aka jikkata wasu da dama arikicin zangon kataf a shekarar 1992 inda aka yiwa musulmi da kirsta

kisan gilla da kisan wulakanci basuji basu gani ba kawai don biyan bukatar wasu. Sannan mu kalli abin da yafaru a yankin kudu maso

kudu tsakanin kabilun Ijow da itsekiri aka kashe yara da mata da basuji basu gani ba, badon komai ba sai don bambancin kabila

ya kamata mugane kowannenmu bazabinsa bane ya kasance dan kabilar da yake.

Haka kuma mu duba irin yadda rikicin jos wato jihar pilato yaki ci yaki cinyewa tsakanin musulmi da kirista inda yake neman zama

wani dan karamin yakin dumiyar Najeriya, kusan wannan rikici yafaru kashi kashi kusan yafi cikin yatsu amma har yanzu wutar wannan

rikici bata lafa ba, Kusan tundaga shekarar 2001 jihar pilato tayi bankwana da zaman lafiya, har kawo yau wannan rikici bai lafa ba.

A shekarar 2004 rikicin addini ya fara aukuwa a kauyen yalwa dake cikin karamar hukumar Shandam wanda sanadiyar wannan rikici ne

ya watsu zuwa wasu garu ruwa makwabta irinsu karamar hukumar lantan ta arewa da ta kudu da ma wani yanki na Wase wanda

sanadiyar haka ne wannan rikici ya watsu har zuwa sauran jihohi makwabta irinsu kaduna da kano inda aka halaka dukiya mai dumbin yawa

kuma aka kashe rayuka masu yawan gaske kuma aka jikkata wasu, kusan shi rikici masominsa aka sani amma ba'a san karshensa ba,

kusan wannan rikicin da ya samo asali daga kauen yalwan shandam shi ne ya sake barkewa ashekarar 2006 inda a sanadiyar wannan rikicine

dubban jama'a suka rasa rayukansu da dukiyoyinsu.

Kusan rikicin da yafi kowanne kazanta shi ne wanda ya faru a shekarar 2008 wanda ya samo asali daga zaben karamar hukumar Jos ta arewa,

inda daga rikicin zabe ya koma na addini kuma kusan wannan rikici da ya auku shiryayye ne domin ko shakka babu musulmi suke da rinjaye

a wannan karamar hukuma ta jos ta arewa kuma inda zakasan abin da makirci ya mai karatu hukuma sai ta sanya ranar zaben ta kasance ranar

Alhamis inda za'a wayi gari juma'a ranar da musulmi ke fitowa sallar juma'a inda aka hallaka musulmin da basuji ba basu ganiba inda asanadiyar

wannan rikicine 'yan sanda suka binne gawarwaki 426 a rami daya bayaga biliyoyin dukiyar da aka rasa da kuam dubban motocin da aka kona

bayan wannan wani rikicin ya sake barkewa a Dutse-Uku duk a karamar hukumar jos ta arewa, a sakamakon wani mutum da yazo maida

gidan da aka kruguza masa kiristoci suka farmasa a wani kaulin kuma sakamakon wasan kwallo da wasu musulmi sukayi a harabar wata coci,

wallahu a'alam, baya ga wannan rikici na watan nuwamba a wannan shekarar ta 2008 wani rikicin ya sake barkewa wanda kuma ya kazanta inda 'yan sanda sukace sun kirga gawarwaki 362 a yashe akan titi, haka kuma anyi ta ganin wasu gawarwakin musamman a garin Digo na Hauwa inda akaringa ganin gawa acikin rijiya da shadda da gurare marasa kyan gani. Haka kuma babu wanda zai iya kiyasta adadadin mutanen da suka rasa ransu a karamar hukumar Riyom da kuma Dogo na Hauwa.

Baya ga wannan kuma ga kisan mummuke da akeyi da kuma dauki day-day aciki da waje garin jos inda zaka ga wani akwata wani rijiya wani

ma yashe kan titi. Abin tambaya anan shine me yasa a yankin jos ta arewa ne wannan rikici yafi faruwa. Anan ina ga ya kamata gwamnati tayi

duba na tsanaki dan gane da abin da yafi dacewa da jihar pilato idan rabata shi ne mafi alkhairi to babu jira abinda ya kamat ayi kenan.

Kuma me yasa najeriya tayi kaurin suna wajen rikicin addini da na kabilanci shin mukadai ne kabilu da yawa mukadaine muke da bambancin Addini.

Malamai sun sha yin wa'azi a masallatai, haka kuma acoci anshayin irin wannan wa'azi cewaDuk Addinin Musulunci dana kirista babu wanda yake umarni da kisan ran da bataji bata gani ba. Kuma musanifa Dukiyoyin mu ne muke halakawa wanda mukayi wahala wajen tarawa, tayaya muna halaka dukiyoyinmu da kanmu kuma zamu kirawo masu saka jari kasarmu shin su mahaukata ne basa sin dukiya ne.

Mafita shi ne muji tsoron Allah mu koma ga Allah duka musulmi da kirista, kuma yaka mata gwamnati ta hada kai da kungiyoyi irinsu spreme council

for Sharia in Nigeria da Jama'atu nasrul islam da crristian Association of Nigeria da kuma masu rike da sarautu da malaman addini wajen kawo

karshen wannan rikici. Allah ya zaunar da kasarmu lafiya ya bamu karuwar arziki da wadata Amin.

Yasir Ramadan Gwale

Shugaban kungiyar muryar Talakawan

Najeriya reshen jihar kano.

07028690570

No comments:

Post a Comment