Sunday, November 27, 2011

Waiwaye Adon Tafiya: Rayuwar Bahaushe Ada Da Yanzu

Waiwaye Adon Tafiya: Rayuwar Bahaushe Ada Da Yanzu

Ya dan uwa mai karatu ina mai yimaka godiya da ka samu zarafin karanta wannan mukala tawa, Allah ya sa mu dace amin. Ko kasan rauwar malam Bahaushe a lokutan baya da suka gabata rayuwace mai ban sha’a kwarai da gaske domin tundaga Burgu har zuwa yahuri duk inda kaga malam bahaushe halinsu daya wajen tausayi da amana da biyayya da kamun kai ga kuma taimakon junansu.

A taikaice ya mai karatu Bahaushe kusan dukkan kabilun kasarnan babu wanda ya kaishi gaskiya da amana, wannan tasa kowacce kabila ta ke son hulda da malam bahaushe ba don komai ba sai don tsare gaskiya da girmama abokin zamansa. A lokutan baya wannan tasa ko kasuwanci za’a kulla tsakanin kabilu akan nemi malam Bahaushe ya zama shaida domin ana da yakinin bazaiyi ha’inci da rashin amana ba.

Zaka yarda dani idan ka kalli yadda baki daga kasashen waje idan suka zo nageriya sukan so su zo kasar hausa, misali shuwagabannin kasashe da yawa sun kawo ziyara nageriya amma duk wanda yazo nageriya bai zo kasar hausa ba to ka gayamasa tabbas yana da sauran kallo. Shugaban kasar zambabuwe Robert Mugabe yazo kasar hausa har cikin fadar sarkin kano haka tsohon shugaban kasar Tanzaniya wato julios Nyarere da kuma Shugaba yuwairi musabveni na Uganda, dama kar kayi maganar kasashen Ghana da nijar da sudan da kamaru da benin kusan wadan nan kasar hausa ta zama gida a gurinsu.

Idan kuma muka duba kasashen asiya da kasar turai da amurka dukkan wani shugaba da zai kawo ziyarar aiki nageriya yakanso yazo kasar hausa ba don komai ba sai irin yadda suke samun labarin mutanen cikinta. Idan ka dauki kasar ingila kusan zamuce kasar hausa gidace agaresu.

Wani abain ban sha’awa da rayuwar malam bahaushe har gaiyatarsa akeyi zuwa sauran kasashen duniya, badon komai ba saboda rayuwarsa abin sha’awane saboda me yana da kula da al’adunsa aduk inda ya tsinci kansa domin kuwa zaka ga malam bahaushe da sanye da babbar riga da hula da carbi a hannunsa a tsakiyar birnin landan wannan yakan baiwa turawa da yawa sha’awa ta yadda zakaga suna yawan daukar hota dashi. Ya ishi malam bahaushe alfahari shi ne an gaiyyaci hausawa kusan 42 zuwa ingila a shekarar 1897 domin su taya sarauniyar ingila Victoria muranar cikarta shekara 60 abisa gadon sarauta, ko shakka babu wannan wani abune da tarihi bazai mance da shiba arayuwar malam bahaushe.

Idan ka kalli rayuwa da zamantakewar malam bahaushe ta yadda yake kula da makwabtansa tayadda zaka samu malam bahaushe yana cin abinci musamman na dare da makwabtansa, hakana malam bahaushe yakan hada yaran makwabta ya yi masu kaciya ko asanyasu makaranta tare wannan ko shakka babu zamantakewa ce mai kyau. Tayadda wasu musamman turawa mutum zai shekara baice da makwbcin bihin ba, amma idan ka dauki rayuwarmu idan makwabcin ka ya kwana uku bai ganka ba sai ya tambaya anya wane lafiya kuwa kwana biyu bana ganinka. Wannan tasa ko acikin gaisuwar malam bahaushe zakaji ykan kula da makwabcinsa ta hanyar tambayarsa ya iyalinka kuna lafiya, da sauransu wannan tasa naga wani abin mamaki lokacin da muka gaisa da wani balarabe sai na ce ya iyalinka sai yace kaico ina ruwanka da iyalina, ni kuwa na bashi hakuri nace Allah sarki malam bahaushe rayuwarka abinkoyi.

Haka kuma idan ka dubi abokan zamanmu wato yarabawa da inyamurai zaka ga a idiyaraba bayerabe ya dauki malam bahaushe aiki a matsayin mai kula da sashin kudi wanda ko amafarki bazai taba daukar inyamuri ya bashi amanr kudi ba haka abin yake idan kaje abbah idan zaka iske inyamuri ya dauki bahaushe aiki yana kuma kula masa da dukiyarsa bai dauki inyamuri dan uwansa ba, wannan karara ya nuna irin yadda malam Bahaushe yake da amana a wancan lokacin kuma duk inda akaga malam bahaushe da shigarsa ta hausawa zakaga yadda ake girmamasu.

Na taba jin wani dan jaridar Radiyo nageriya Kaduna wato halilu getso yace ya sauka a filin jirgin sama na Heathrow da ke landan yace yaje sanye da kayan hausawa da hula da carbi a hannunsa kuma tafiyace bashi kadai ba yana cikin wata tawaga ce amma yace shikadaine ba’a bincika kayansa ba, yace awannan lokacin jami’an tsaron wannan filin jirgi sun girmamashi yace badon komai ba sai yadda suka samu labarin Bahaushe mutumne mai gaskya da rikon amana, yace aka tambayeshi mene cikin jakarka yace ‘yar kukace da yajin daddawa na kawo wa ‘yan uwana tsaraba sai kuma ‘yan tsummokarana. Yace haka nan ya wuce amma sauran abokan tafiyarsa dake kabilu daban daban ne sun sha tambayoyi da bincike.

Wannan tasa malam bahaushe ya cirri tuta domin dukkan kabilun kasarnan babu mutumin da ake girmamawa bilhakki kamar malam bahaushe kuma ciki da wajen nigeriya duk inda akaga malam bahaushe ana yimasa kallon wani mutum mai amana da gaskiya da adalci awancan lokacin.

Kamar yadda nace waiwaye adon yafiya sai kawaiwaya baya kaga yadda kake sannan sai kayi tunanin gaba me yakamata kayi. Ko shakka babu yanzu rayuwarmu bah aka take ba yanzu za’a hada baki da mista bahaushe ayi yaudara da ha’inci da makici kala-kala, sannan malam bahaushe ya zama mutum mai buri da yawa ga son taro dukiya mai dimbim yawa ta kece raini da auren mata barkatai ga son gina gidaje ko ina amma kuma ko kadan bamu son shan wahala ko ta sisi. Shin taya zamuyi mu dawo da martabar da akasan malam Bahaushe awancan lokacin mai karatu kalubale gareka.

No comments:

Post a Comment