Tuesday, March 1, 2016

Ana Fakewa Da Guzuma . . .


ANA FAKEWA DA GUZUMA . . .
Bayan da asirin su Malam Ibrahim Zakzaky ya tonu, kuma Allah ya kama su ta hanyar turo musu da Sayyid Ayatollah Buratai Yusuf ya darkake su darkakewa. Muna fatan abinda ya samesu na wannan jarabawa ya sa masu hankali da fahimta daga cikinsu su fahimci gaskiya su karbeta, su gane turba ta gaskiya su kama Sunnar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam su daina Shiah domin b'ata ce mabayyaniya. Muna fatan abinda ya same su ya zama ukuba anan duniya ga duk masu zagi da aibata Iyalai da abokan Ma'aiki Sallallahu Alaihi Wasallam.
Da yake macizai ne basa gina rami da kansu, sukan fake da guzuma su sari karsana. Su dai sun san karyarsu ta sha karya ba zasu iya fitowa fili su zagi ko Aibata Sayyadi Ayatollah Burtai Yusuf ba, a dan haka sai suka fake da siyasa suna zagin Shugaban kasa sabida da d'an siyasa ne.
Shugaba ko wane iri ne yana da kima da daraja a Musulunci, haka kuma zaginsa fasikanci ne. To amma su dama suje nema dan su yiwa shugaban kasa tatas, su amayar da miyagun maganganun akansa. Dan haka daga zarar wani yayi maganganu na suka ko hamayya da Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari sai su fake da wannan suyi ta zagi da cin mutunci. Alhali kuma su din turbar siyasa Dagutanci ne a wajensu balle muce su shigo fagen siyasa a buga da su.
Hamayya ko kalubalanta a siyasar Demokaradiyyar da Shiah suka kafirta Halal ne. Mun gamsu, mun kuma Amincewa da haka, cewar a kalubalanci Gwamnati kuma ai mata hamayya. Amma su 'yan Shiah abinda suke yi ba haka bane. Suna amfani da damar 'yan hamayya suna cin zarafi da mutuncin Shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Allah ka nuna mana gaskiya mu fahimceta kuma ka bamu ikon binta. Ka nuna mana karya kamar yadda ka nuna Mana Shaianci mu gane karya ne ka bamu ikon kauce mata, kamar yadda muka kaucewa Shiah kuma muke neman tsari da ita. Allah ka taimaki kasarmu ka bamu lafiya da zaman lafiya.
Ya Allah kasa wannan abun da Sayyid Ayatollah Buratai Yusuf yayi shi ne silar kawo karshen duk wani makirci da makida ta 'Yan Shiah gurbatattu lalatattu. Allah ka kare kasarmu daga maguanci da kafircin Shiah.
01-03-2016

No comments:

Post a Comment