Thursday, March 3, 2016

Mayar Da Ese Oruru Gaban Iyayanta Shi Ne Abinda Ya Dace


MAYAR DA ESE ORURU GABAN IYAYANTA SHI NE ABINDA YA DACE

Ni kam banga wani abin tashin hankali dan an mayar da wannan yarinyar gaban iyayanta ba. Iyayan ta mahaifa suna da hakki akanta, dan haka ba wani abin tayar da jijiyar wuya bane dan an mika musu ita. Rayuwar Musulmi cike take da abin koyi, ga duk wanda ya fahimci darussan da ke cikin SULHUL HUDAIBIYYA da mayar da sahabi Abu Jandal Ibn Suhailu Ibn Amri r.a da Annabi Sallallahu Alaihi Wa Sallam yayi ga iyayen sa mushrikai a tsakiyar sulhun, na meye nasa zai tayar da hankali dan an ce yarinya ta koma ga iyayanta? 

Addinin Musulunci na Allah ne, kuma da kaddarawarsa ne Subhanahu Wata'ala, komai yake tabbata. Wannan yarinya da ta Musulunta, indai ta Musulunta don Allah da neman yardarsa, Allah zai bata kariya a duk inda take. Haka kuma, a Musulunci komai yana da ka'ida da kuma sharadi. Babu yadda za a ce mutum ya dauko 'yar mutane ya aureta ba tare da sanin iyayanta ko da amincewar shuwagabanni ba kuma ace auren ingantacce ne. 

Ni ina ganin indai ba tsananin zafin kai da kafiya ba, ai wannan lamari mai sauki ne. Tunda yarinya ta koma gaban iyayanta, sai shi yaron yabi hanya sahihiya dan neman aurenta a wajen waliyyanta. Ba yau aka fara yin aure tsakanin mutanan kudu da Arewa ba, ba kuma yau ne Musulmi suka fara auren wanda ba Musulmi ba su musuluntar da su. Jiya naji Malam Aminu Daurawa yayi bayani gamsasshe akan wannan batun. Allah ya bamu lafiya da zaman lafiya. Ya Allah ka cigaba da baiwa addininka kariya.

Yasir Ramadan Gwale 
03-03-2016

No comments:

Post a Comment