Thursday, February 4, 2016

Ziyarar Da Na Kai Cibiyar Addinin Musulunci Ta Al'umma Dake Garin Baltimore


ZIYARAR DA NA KAI CIBIYAR ADDININ MUSULUNCI TA GARIN BALTIMORE

Daga Barack Obama

A yau, cikin ikon Allah na samu zarafin kai ziyara ga katafariyar cibiyar addinin Musulunci ta al'umma dake garin Baltimore. Naga Masallaci inda dubban Musulmi Amerikawa ke haduwa da juna da iyalai dan gudanar da Ibada kamar ko wane irin Masallaci a Amurka, cibiyar waje ne inda dangi da makwabta kan hadu tare da juna suna gudanar da ayyukan Ibada na addini, ga makaranta da yara kan koyi Ilimin addini da zamantakewa, sannan ga sashin bayar da agajin gaggawa, naga mutane da dama da suka bayar da lokacin su kyauta domin aikin hidimtawa al'umma.

Wannan ziyara tawa, wata muhimmiyar dama ce a wajena da zan ganewa ido na yadda Musulmi ke aiwatar da alamuransu na addini, sannan na karfafa musu guiwa wajen taimako da ayyukan sa-kai, sannan kuma na tuna musu cewar Musulmi da yawa sun bayar da gudunmawa mai dumbin yawa a baya domin ciyar da wannan kasar tamu gaba. Kuma wannan ne Babban dalilin da yasa kasarmu abin alfaharinmu ta daukaka a duniya, domin kowanne dan Adam yana da 'yanci da kuma ikon yin addinin sa.

Al'ummatai da dama na Musulmi musamman daga cikin Manoma da 'yan Kasuwa da masu sana'o'i da dama suka taimaka wajen gina tare da bunkasa habakar wannan kasa tamu. Su ne suka taimaka wajen ilmantar mana da 'ya 'yanmu, da yawansu daga masu aikin jiyya da likitoci sun hidimtawa al'umma a wannan kasa ta Amurka. Wasunsu da dama sun samu lambobin Yabo bisa wasu ayyuka da suka na bajinta, ciki kuwa har da karbar lambar Yabo ta zaman lafiya wato Nobel Peace Prize.

Haka kuma, dumbin matasan Musulmi Amurkawa sunyi abubuwa na bajinta da suka Shafi fasaha da kimiyya da kirkire kirkire. Wannan ce ta sanya a koda yaushe mukan hadu domin nuna jinjina da godiya ga irin wadannan matasa, daga cikinsu kuwa, akwai irinsu Mohammed Ali da Kareem Abdul-Jabbar, wanda suka sanya farin ciki da annashuwa da dama a zukatan al'ummarmu. Daga cikin Musulmi a Amurka akwai, 'yan kwana-kwana wanda suke sadaukar da rayuwarsu dan kashe duk wata gobara. Sannan ga kuma 'yan sanda mata da maza wanda suke aiki tukuru dan kasarmu.

Yanzu haka, Musulmi da dama anan Amurka na cikin zullumi da damuwar taka musu hakki ko cin zarafinsu. Iyaye da 'ya 'ya na ta karakaina cikin tsoron taka musu martaba da mutunci, to ya ku ina mai tabbatarwa da duk wani Musulmi a Amurka ba Baltimore kadai ba cewar mu duka Amurkawa ne, kuma mu al'umma daya ne, dan haka duk wanda zai kaiwa Musulmi hari anan to ya sani mu duka gaba dayanmu ya kaiwa hari.
Dan haka, duk wani tsagera ko mara kunya da zai ci zarafin Musulmi akan addinin sa to ya sani ya shirya fada da mu ne baki daya, kuma zamu tsaya kai da fata wajen ganin bamu bari anci zarafin Musulmi a Amurka ba, kawai dan sunce su Musulunci zasu yi. Haka nan kuma, zamu yi fatali da duk wani tsarin siyasa da zai cuzgunawa Musulmi, zamu yi magana da murya daya, ba tare da mun cutar da wani ko wasu al'umma ba akan addinin su. Kuma yana da kyau duknamu mu sani cewar gaba dayanmu daga Allah muke kuma gareshi zamu koma.

A saboda haka, ina amfani da wannan dama na tabbatarwa da dukkan Musulmin Amurka maza da mata cewar, kowannenmu yana da iko da 'yancin da doka ta bashi a matsayinsa na dan kasa. Ku din nan ba wai kawai Musulmi bane ko Amerikawa a'a ku Musulmin Amerika ne, kuna da cikakken 'yancin yin walwal karkashin koyarwar addinin Musulunci. Na gamsu kuma na yadda, al'ummar Musulmi a Amurka mutane ne masu zaman lafiya da fatan Adalci ga kowa.

Wannan shi ne dalilin kawo muku wannan ziyara domin na karfafa muku guiwa, ku sami yakini akan abinda kuka yi Imani da shi, babu mai cin zarafinku sabida addini mu zuba masa ido. Dan haka, idan muka cigaba da kasancewa al'umma daya, zamu sami karfi kuma rauni ba zai riskemu ba. Dole ne kuma mu mutunta bukatun juna. Na gobe, shukran.

Yasir Ramadan Gwale
04-02-2016

No comments:

Post a Comment