Wednesday, March 11, 2015

Shin Za Ayi Zaben 2015 Kuwa?


SHIN ZA AYI ZABEN 2015 KUWA?

Sau da yawa lamura musamman na siyasa a Najeriya daga jita-jita suke zama gaskiya. Ina zaton batun d'aga zab'e daga Fabrairu zuwa Maris duk daga jita jita muka dinga ji har ya zama gaskiya, wannan abinda yake nunawa shi ne, a wannan babban zaben "interest" na masu mulki ne kawai ke aiwatuwa, ko al'umma sun yarda ko basu yarda ba.

Ya isa abin misali, ace anyi Babban Taron Manyan Masu Ruwa Da Tsaki Na kasa 'Council of State' aka ce babu batun d'age zabe daga Fabrairu, a wajen wannan taron duk wani 'who is who' a Najeriya ya halarta, aka tabbatar da cewa zab'e yana nan daram dam dam, har Shugaban hukumar zab'e Attahiru Jega ya tabbatarwa da taron cewar hukumarsa ta shirya tsaf domin gudanarda zabe a Fabrairu, 'yan Najeriya akai ta shewa.

Kwatsam kwanaki kad'an bayan wancan taro na copuncil of state, sai gashi hukumar zabe ta hannun Farfesa Jega da ya tabbatarwa da Council of State cewar zasu yi zabe a Fabrairu babu wata matsala, sai gashi ya bayar da sanarwar jingine zabe daga Fabrairu zuwa Maris da Afrilu! Ya akai haka ta faru? Ko da ba'a san da matsalolin da aka jingina da su bane? Wannan sanarwa haka tazo bagatatan, kuma ta zauna daram dam cewa an d'age zabe kuma ya d'agu. Amma a zahirin gaskiya, da yawan 'yan Najeriya sun kwana da sanin cewar dage zab'e ra'ayi ne na Gwamnatin Tarayya, domin maganar d'agawar ta fara samo asali ne daga Kanar Sambo Dasuki.

Bayan wannan sanarwa, Attahiru Jega ya shawa 'yan Najeriya alwashin cewar daga wannan d'agawar ba za'a kuma yin wata ba, zab'e sai anyi shi a Maris da Afrilu, kamar ba Jega ne yace sun shirya tsaf dan yin zabe a Fabrairu ba! A hakikanin gaskiya, dangane da wannan zab'en, ra'ayin gwamnati shi ne a sama, idan har da gaske Gwamnatin Najeriya na san ayi zabe to ba makawa za'a yi shi, idan kuma ya tabbata cewar bata son ayi zabe, to hakan Jega zai bayar da wata sabuwar sanarwa, idan yakai lokacin kenan.

A bayyane take cewar idan an sake d'age zab'e daga Maris, to za'a shiga rud'ani, sabida abubuwa zasu cakudewa tsarin Mulki, dan masu fashin ba'ki na cewa kundin tsarin mulki yace Tilar ayi zab'e kwanaki 30 kafin 29 ga watan Mayu, haka kuma, kundin mulkin Najeriya bai yi wani tanadi ba dangane da gwamnatin rikon kwarya ba a cewar masana. To idan aka d'age zab'en meye zai faru?

YASIR RAMADAN GWALE​
11-03-2015

No comments:

Post a Comment