Sunday, March 8, 2015

Ranar Addu'ah


RANAR ADDU'AH

Turawa sun ware ranar yau a matsayin ranar addu'ah, amma mu al'Umar Musulmi kullum cikin addu'ah muke da rokon Allah ya bamu daga cikin falalarsa Subhanahu Wata'ala. Ranar wata Juma'a naga tasiirin addu'ah wallahi. Ranar na tashi na tafi Masallaci da wari kuma a lokacin bani da kudi haka na tashi, bayan da na isa Masallaci nayi Nafila zan zauna kawai sai na hangi wani mutum ya daga hannu yana addu'ah, sai ya tunasar da ni, kawai nima na daga hannu zan yi addu'ah, abinda ya fara zuwa raina a lokacin shi ne wani mutum da nake bi kudi amma ya daina yi min waya. Kawai sai nayi addu'ah nace Ya Allah ka baiwa wane kaza ikon biyana kudina, nayi sauran addu'o'i na gama. Wallahi abin mamaki banyi minti biyar da yin addu'ar nan ba kawai sai wayata tayi kara, kamar ba zan dagaba, amma na make murya na daga wayar, kawai sai ji nayi yace Malam Yasir wane ne yake magana dan Allah ka gaya min inda zan tura maka kudin ka! Nan take nayi Sujjada na yiwa Allah godiya, nan fa na dinga zabga addu'ah ba kakkautawa. Ba shakka dukkan abinda bawa yake nema idan ya dirfafi addu'ah tare da kyauta tawaga Allah zato ba shakka zai sameshi ko meye. Shi yasa yanzu bana tsoran kudina su shiga hannun wani su makale, dan da adduah zan bishi. Allahumma Taqabbal Minna Du'a'ana .

Yasir Ramadan Gwale 
06-03-2015

No comments:

Post a Comment