Wednesday, January 15, 2014

Idan An Girma Asan An Girma!!!

IDAN AN GIRMA ASAN AN GIRMA

A shekarunsa yayi 'da da ni dan ba shakka ko bai haifeni ba, to, ya haifi kanina. Sau da dama idan na ga sakonsa ko comments dinsa yana zagina sai abin ya bani mamaki, domin mutum mai shekaru irin nasa ya tsaya yana zagin mutum kamar Yasir Ramadan Gwale mutumin da ya kusa haifa, zagi irin na batsa wanda ko yaro kaji yana yi ka kauda kanka dan kunya amma babba da shi a she babban kwabo ne shi, girma gareshi babu hankali da tunani irin na manyan mutane. Ko kusa zaginsa bai taba damuna ko ya bata min rai ba, domin dubunsa sun zageni a facebook ko tankawa banyi ba balle naji haushi, illa iyaka mamakin da nake yadda ya yasar da sheakrunsa a banza yana zagi da aibanta Yaron da ya kusan haifa. Ban taba mayar masa da martanin zagi ba kamar yadda yake yi min, saboda ko babu komai ni ina girmama farin gashi da tarin shekaru ko da kuwa na banza da wofi ne irin nasa, ballantana kuma mu AHLUSSUNNAH bamu da tarbiyyar duddurawa mutane ashariya. Duk da sanin cewa zagi ba shi da makaranta kowa zai iya yinsa idan yaga dama.

Amma idan na tuna yadda suke zagi da aibata Sahabbai da Matan Manzon Allah SAW, sai na ce to kuma waye Yasir idan ya zageni, mutumin da ya zagi mutanan da suka fi Ubansa da uwarsa da dukkan danginsa daraja! Dan haka, ni zai yi min dadi a raina ace iyayena yake zagi akan ya zagi Sahabbai da Matan Manzon Allah SAW.

Kamar yadda kowane mai hankali ya sani ne, zagi da cin mutunci da aibantawa ai na mutumin da ba shida wata hujja ne, ba shi da wata mafita illa ya yi zagi ya tayar da kura, wanda a ganinsa hakan ita ce dabara ta karshe da ta rage masa wadda zai karkatar da hankalinka daga zahirin gaskiya zuwa wani abu daban.

Wannan mutum ba kowa bane illa wani da ake kira Ashiru Nana. Ina masa fatan Allah ya shiryeshi ya ganar da shi hanya ta gaskiya. Allah ka nuna mana gaskiya gaskiya ce ka bamu ikon binta, ka nuna mana karya karya ce ka bamu ikon guje mata.

YASIR RAMADAN GWALE
15-01-2014

No comments:

Post a Comment