Sunday, January 27, 2013

KADA KA TABA ZATON DAN SHI'AH YANA KARANTA AL-QUR'ANI



KADA KA TABA ZATON DAN SHI'AH YANA KARANTA AL-QUR'ANI 

'Yan Shi'ah duk inda suke suna kokarin nesanta kansu daga Al-qur'ani mai tsarki, basa karanta shi, kuma basa son mai karanta shi, kai hasalima basu yarda da wannan al-qur'anin da mu Musulmi meka karantawa dare da rana ba. Manzon Allah Salallahu alaihi Wasallam shine cikamakin annabawa wanda ALLAH ya turoshi ga dukkan talikai, kuma ya bashi littafinsa (al-qur'ani) wanda yana shafe zanen dukkan wani littafi da ya gabace shi ne. Al-qu'ani zance ALLAH ne da ya turo ta hannun ManzonSa Salallahu Alaihi Wasallam. Shi kuma Manzon Allah ya karantar da al-majiransa Al-qur'ani wato sahabbai, wadannan sahabbai da wadan da suka biyo bayansu sune wadan da suka yi hidima wa al-qur'ani mai tsarki, har ya kawo garemu.

Saninmu ne cewa Shi'ah Mabiya Dan Saba'i suna matukar nuna kiyayya a bayyane ga wadannan sahabban, Kuma shi wannan Alkur’ani Sahabbai ne su ka zo da shi daga wurin Manzon ALLAH Salallahu Alaihi wasallam su kuma ba su yarda da Sahabbai ba. Daga cikin wadan da sukayi hidimar tattara al-qur'ani dan game shi waje guda musamman Usman Bin Affan shine mutum na uku da shi'ah suke kafirtawa, kuma suke matugar gaba da dukkan zurriyarsa da dangoginsu wato banu Umayya, Idan kaji Dan Shi'ah yana zagin Mu'awiyya ko Yazeed wannan kada ya dameka, domin sun sagi wadan da suka fi su Mu'awiya da yazeedu kima da daraja wato khulafu'r Rasheedun Al-mahdiyyen, haka har aka gangaro kan irinsu Sarkin Musulmi Hajjaju Bin Yusuf wanda tarihi ya tabbatar da cewar yayi matukar hidima wa al-qur'ani, domin shine ya sanya aka wasalce al-qur'ani.

Haka Kuma, a lokacin da Al-qur’aninmu ya ke da ayoyi 6236 Kulini daya daga cikin gumakan shi'ah ya ruwaito a mafi ingancin littafan shi’a daga Abu Abdullahi (Daya daga cikin ma’asumai a gurinsu) cewa Al-qur’anin da Jibrilu ya zo da shi ga Muhammad aya 17000 ne” duba (Alkafi, 2/634). Dan haka, Idan ka ji dan shi’a ya na son ya ja hankalinka ya na musanta abin da littafansu su ka fada kuwa, to, ka sani cewa yana takiyya ne, ita kuma takiyya farilla ce a cikin addininsu kamar sallar farilla (Duba littafin Alkafi na kulini 2/217 da Al’amali na Tusi shafi na 229).

A takaice dai ya zama dole a bayyana wa jama’a cewa, addinin shi’a wani addini ne na jabu wanda makiyan musulunci suka taru suka kitsa shi, sannan suka kutso da shi a cikin musulunci da nufin rusa shi, amma abinda basu sani ba Addini na ALLAH ne, kuma shine zai kare kayansa. Kuma su na jingina kansu ga Ahlul Baiti domin su yaudari jama’ar musulmi. Iyalan gidan Manzon ALLAH Salallahu Alaihi Wasallam bayan kuwa barrantattu ne daga akidun shi’a kamar yadda da dama daga cikin magabatansu suka fada.

Dan haka ya dan uwa kada ka rudu da 'yan Shi'ah basu da wata alaka ko ta kusa ko ta nesa da littafin ALLAH al-qur'ani ko addinin ALLAH. Dan ka sake gane haka bari na baka wani misali. A baya yadda masu yin maulidi suke yi, shine akan yi gadan aba'i ko Mimbari yara suna karatun al-qur'ani da karanta sirar manzo, amma yanzu da shi'ah suka silalo cikn lamarin sai suka dauke hankalin mutane daga yin karatun da suke yi a baya, inda suke zaga gari suna kide-kide da wake-wake na batsa. Kaga daga Karanta al-qur'ani ankoma kada bajujala, alhali Manzon ALLAH Al-qur'ani ya zowa da al'ummarsa da shi. To irin haka ne shi'ah suke yin amfani domin raba mutane da addini da kuma al-qur'ani.

1 comment:

  1. mallam me ya faru kwana biyu babu sabuwar kasida. in ce ko lafiya.
    bissalam

    ReplyDelete