Monday, January 9, 2012

Cire Tallafin Mai Fitana Ce Cikin Tattalin Arzikin Kasa

Cire Tallafin Mai Fitana Ce Cikin Tattalin Arzikin Kasa

Yanzu dai kusan za a ce ta faru ta kare dan gane da batun da akayi ta dogon turanci akansa wato batun nan na Fuel Subsidy Removal a turance ko kuma janye tallafin albarkatun mai. Kusan wannan batu shi ne goron sabuwar shekarar da gwamnatin tarayyar Najeriya ta baiwa ‘yan kasa na sabuwar shekarar 2012. Tun da gwamnati ta baiyana wannan aniya tata ta janye tallafin man fetur jama’a da kungiyoyi da masana da talakawa sukayi ta jan hankalin gwamnati akan wannan batu cewa ta janye wannan aniya tata, domin kuwa wannan abu zai jefa talakan kasarnan cikin halin kaka nakayi da kazamin talauci. Tun a wancan lokaci gwamnati tayi hasashen cewa idan aka cire wannan tallafi litar mai zata koma N150 daga tsohon farashi na N65.

Bada wannan sanarwa ke da wuya sai al’amura suka sauya. Inda akayi ta ganin dogayan layuka a gidajen mai nan da nan lita ta d’aga daga N65 har zuwa N200 a wasu guraran. sannan kayan masarufi suka yi tashin gwauron zabi haka ma harkokin sufuri suma duk suka sauya daga tsohon farashi, kai kace dama duk jama’a jira suke gwamnati ta janye wannan tallafi su kwashi garabasa. Kusan wani abun ban haushi da kasarmu shi ne duk lokacin da farashi ya tashi kamar shekarun mutum haka yake ma’ana baya sauka. A tarhin Najeriya saudaya farashin fetur ya taba dawowa baya lokacin marigayi tsohon shugaban kasa Mallam Umaru Musa YarAdua inda daga N70 ya koma N65, wanda wannan shi ne irinsa na farko a tarihin farashin man fetur a Najeriya amma duk da haka kayan masarufi basu dawo daga hawan da sukayi ba.

Da yawan ‘yan Najeriya basu san ma wani abu Tallafin man fetur ba sai da wannan batu na janyewa ya taso. Abin tambaya shin menene wannan tallafin da ake bukata wanda aka ce ana baiwa albarkatun man fetur. Wato tunda kungiyar kwadago ta tursasa gwamnati na biyan sabon tsarin albashi na mafi karanci na N18,000 gwamnati ta ke ta neman hanyoyin da zata samar da wancan kudi domin cika wannan alkawari da ta dauka, don haka ne ta fito da wannan batu na cire tallafi, inda za a samu kudin da zata raba tsakaninta da gwamnoni wanda zasu iya biyan wannan sabon tsarin albashi. Ma’aikatan da basu wuce kashi 5 cikin dari na al’ummar Najeriya ba.

Abin tambaya lokacin da ake baiwa albarkatun man fetur wannan tallafi da ake Magana shin amfitar da talaka daga cikin halin kaka nakayi an maganace al’amuran tsaro da ya damu al’ummar kasarnan an samar da wutar lantarki da ruwan sha mai inganci? yanzu waye zai bugi kirji ya gasgata gwamnati cewa da gaske suke bayan cire wannan tallafi za a inganta rayuwar talaka. Wadan nan mutanan da suke rike da madafun iko kafin cire wannan tallafi sune dai haryanzu don haka wannan wani wasan kwaikwayo ne kawai, cewa za a inganta rayuwar talaka bayan cire wannan tallafi babu wani abu da zai canza, tunda shekara 13 da PDP tayi akan mulki bata iya samarwa da ‘yan Najeriya tsayayyar wutar lantarki ba duk da karairay da kumfar baka da akayi ta mana, da kuam irin dimbin dukiyar da aka ce an kashe.

Abin tambaya wai shin gaba daya adadin lita nawa ne ake bukata na al’barkatun mai domin ‘yan Najeriya suyi amfani dashi na fetur da kananzir da man dizal da dangoginsu? Sannan akwai abin da ake cewa “domestic allocation” wato wani abu da ake bayarwa na gurbataccen man fetur din da aka hako shin menene adadin da ake bayarwa saboda wannan? Sannan kuma har ila yau acikin adadin matatun man fetur din da muke da su guda 4 wanne adadi suke bukata na shi wannan allocation domin suyi amfani dashi su tace manfetur da dangoginsa? Shin suna tacewa ko yana saura, kuma idan ya yi saura me ake yi da ragowar? Sannan kuma idan za a shigo da man fetur daga waje a nawa ne ake kashewa kafin da bayan zuwansa kasar nan?

Har wa yau kuma menene rarar da ke tsakanin abinda Najeriya ta ke sayarwa domin ‘yan kasa da kuma abin da ake kawowa daga waje? A ganina sai anyi wannan kididdiga ne sannan zamu gane abu kaza ne muke bukata na shi wannan tallafi, ba wai kawai ayi ta mana dodorido da sunan tallafi ko janye tallafi ba. Kuma wannan abin shi ne yake nuna cewa akwai badakala mai yawa a harkar da ta shafi NNPC domin idan zamu iya tunawa a lokacin gwamnatin Olushegun Obasanjo karkashin mai bashi shawara a harkar manfetur Alh. Lurwanu Lukman ance ambada lasisin kafa sabbin matatu guda 18 ina batun ya kwana?

Sannan wannan batu babu abinda zai kawo sai fitina cikin sha’anin tattalin arzikin kasa, domin indai gwamnati akeyi ta Demokaradiyya ‘yan Najeriya sunce basu yarda ba da wannan aniya ta gwamnati ta janye tallafi. Kuma ita gwamnati bata yiwa al’umma bayani na gaskiya ba akan wannan batu sai kawai gwamnan babban Banki da minister kudi ne suke ta lankwasa harshe akan wannan batu da ‘yan Najeriya sun kasa fahimtar shin wannan tallafi akwaishi ko babu shi, domin wannan abun yana da sarkakiyar gaske, ita kuma gwamnati tana ta yiwa ‘yan kasa kafar angulu.

Kuma idan har da gaske wasu ‘yan tsiraru ne suke amfanar wannan tallafi shin su wane su harda gwamnati ta kasa daukar mataki akansu. Naji mamaki kwarai da gaske lokacin da gwamnan babban Banki yake bayanin cewa manyan mutanenen suke amfanar wannan batu me gwamnati ta keyi da bazata iya fitowa ta kalubalanci wadan nan mutane ba da suke ci da gumin talaka.

Kuma kamar yadda mukaji masana na sharhi akan wannan al’amari taya za a dauki kudinka ayi maka bukata sannan kuma ace wai ambaka wani abu wai shi tallafi ta ina. Bayan dukiyar kasa ce kuma ta al’ummar kasa ce. Kuma idan da gaske gwamnati ta ke mutanan da suka mallaki rijiyoyin man fetur a ina suka samu uban wa ya basu a ina suka gada? Ta kwace su ta dawowa da talakawa hakkinsu mana idan da gaske suke, sannan bayan haka muna sane da yadda akace duk gangar danyan man da aka hako wadan can miyagu azzalumai suna da wani kamasho aciki.

Kasan cewar babu wani yare da gwamnati take saurin fahimtarsa kamar zanga-zanga wannan tasa kungiyoyi sukayi amfani da wannan dama domin shirya gangami na lumana don nuna bacin ransu akan wannan batu. Kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada Kuma Alhamdulillah kusan tun farkon wannan zanga-zanga da aka fara daga Ilori har zuwa kano, kaduna, Abuja, legas, Ibadan, sokoto da sauransu duk babu inda aka samu rahoton ‘yan zanga-zanga sun tayar da hankali hasalima sai dai amfani da jami’an tsaro da gwamnati tayi don muzguna musu musamman a Ilori da Kano inda rahotanni suka ce an kashe mutum biyu tare da raunata daruruwa, da lalata ababen hawa na dalibai da kungiyoyi.

Hakika ansha ankarar da gwamnati cewa irin abin da yake faruwa a kasashen larabawa da akwai yiwuwar zai faru a Najeriya. Allah ya jikan sheikh Ahmad Lemu badan ya mutu ba sai da ya ankarar da gwamnati acikin rahoton da ya mika na musabbabin rikicin bayan zabe. Kuma da alamar abinda ya yi awon gaba da Husni Mubarack a Egypt da Zainul Abiden Ben Ali a Tunisiya da kuma wanda ya yi sanadiyar mutuwar Kanal Gaddafi shi ne zai faru a Najeriya. Hausawa dai sunce a juri bara wai albasa far ace.

Yasir Ramadan Gwale

Yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment