Saturday, January 21, 2012

Shin Idan Nayi Zina Laifin Nawa ne ko na Mahaifina?

Yabo da godiya da kirari sun tabbata ga Allah ubangijin talikai, tsiransa da amincinsa su kara tabbata ga fiyayyan halitta babban Fatima cikamakin annabawa Annabi Muhammad salallahu alaihiwasallam da alayansa da sahabbansa da wadand sukabi tafarkinsu har ya zuwa ranar sakamako. Ina shaidawa babu abin bauta bisa cancanta sai Allah kuma annabi Muhammad bawansa ne manzonsa ne. dukkan wanda Allah ya shiryar shi ne hakikanin shiryayye, haka kuma dukkan wanda Allah ya batar babu mai iya shiryar da shi.

Hakika yanzu muna cikin wani yanayi mai cike da tashin hankali da firgici da ban tsoro. Zaka yarda dani ya dan uwa mai karatu cewa wannan lokacin yana cike da kalubale mai yawan gaske, kalubale ta kowane fanni na rayuwa. Kayiwa Allah godiya idan ka samu kanka cikin masu aikata alkhairi da kuma kokarin kaucewa munanan ayyuka wadan da suke kaiwa izuwa ga fushin ubangiji, kamar zina da dangoginta. Ya mai karatu ina fatan zaka bani aron lokacinka tare kuma da fahimtata dan gane da wannan maudu’I, babu wani abu mai ban mamaki dangane da taken wannan mukala.

Ko shakka babu, yana daya daga cikin kalubalen wannan zamani shi ne kowane uba yana son yaga dansa ko ‘yarsa ya/ta samu ilimi ingatacce. Wanda wannan ilimi shine silar ginuwar rayuwar kowane mutum a wannan lokaci. Wannan ce ta sanya iyaye kan baiwa ilimin ‘ya ‘yansu kulawa ta musamman da kuma fatan watakila zasu zama wasu a nan gaba. Tabbas kusan duk wanda kaga ya zama wani abu to tabbas karatu yana daga cikin sila, Domin da karatu ne dan adam kan kai kololuwarsa ta kamala.

Irin wannan kalubale ne yakansa duk da soyayyar da iyaye ke yiwa ‘ya ‘yansu su daukesu su kaisu garuruwa masu nisa domin samun ilimin da zai yi musu linzami a rayuwa da samun kyakkyawan yanayi. Shakka babu iyaye na da gudunmawa me yawa da zasu baiwa ‘ya ‘yansu wajen ganin sun zama mutane na gari, domin sudin makiyayane akan abin da damansu ya mallaka.

Ya dan uwa shin ko kana da labarin rayuwar da akeyi a makarantun gaba da sakandare ko jami’a. hakika rayuwar jami’a wata irin rayuwa ce mara misaltuwa cikin dan gajeren lokaci. Da yawan iyaye kan so ‘ya ‘yansu su je jami’a domin karatu, amma kuma da yawa basu cika bibiyar wace irin rayuwa ‘ya ‘yansu sukeyi acikin jami’a ba. Hakika rayuwar ‘ya ‘yanka tana cikin hadari musamman mata, Ina fatar zaka yarda dani, domin yanzu rayuwar mata a jami’a ta zama abin tausayi matuka. Mafiya yawan ‘yan mata kanso suyi aure bayan kamala jami’a a yayin da suke dokin shiga jami’a amma ba’anan gizo yake sakarba sai bayan sun kamala suke gane ashe sunyi kuskure!

Yanzu makarantun jami’a sun zama wani abin tsoro ga dukkan wani uba mai kishi. Domin bawai kawai karatun da kasani ba dalibai suke koya harda wasu munanan halaye wadan de ke cigaba koda bayan sun gama makaranta. ‘Yanmata da yawa na fadawa cikin wani mawuyacin hali na bala’in zina da dangoginta a jami’a, yanzu ansamu wasu muggan kungiyoyi acikin jami’o’I wadan da ke kokarin kauda budurcin ‘ya ‘ya mata ta kowane irin hali, wannan ta sanya akan hada baki da wasu muggan malamai wadan da ke kada dalibai mata jarabawa ba dan sun cancanci su fadi ba kawai sai domin neman wata dama da za’a nemi daliba ta bada kanta domin bata mata rayuwa.

Wannan ta faru a kusan dukkan jami’o’inmu ba sau dayaba ba sau biyu ba. Idan zaka ga wani abin bakin cikinma harda matan aure ake kokarin jefawa cikin irin wannan mummunan tarko. Yanzu makarantun jami’o’I sun zama wata kafa ta yada muggan dabi’un nan na mata masu neman junansu ta kowane hali, kusan mafiyawa daga cikin daliban jami’a suna da masaniya akan wannan batu.

Hankalina ya jawu kan rubuta wannan mukalane sakamakon wani kaset na wa’azi da marigayi shekh Jafar Adam kano ya yi a Maiduguri ta jihar Borno, wato karatun tafsiri da yake gabatarwa dukkan watan azumi. A lokacin da mallam ke karatu cikin suratu Tauba wata daliba ta rubuto masa wasika daga jami’a akan wani mawuyacin hali da ta shiga, sakamakon iyayanta sunce sai tayi karatun jami’a sannan tayi aure ita kuma tanada burin tayi aure kafin ta shiga jami’a amma iyayanta suka kekasa kasa suke ce ba haka ba. Wannan ce ma ta sanya na ari kalmominta wajen gina kanun wannan muqala. Kamar yadda ta rubuta a karshen takardar da marigayi shekh Jafar Adam ya dauki lokaci maitsowo yana karantawa. A cikin wasikar da ta rubuta tayi bayanai masu cike da tashin hankali wanda duk wanda ke da ‘ya da take a jami’a dole hankalinsa ya tashi, domin tace akan yi kokarin yaudarar yarinya da kudi da wasu kyale-kyale a karon farko idan kuma ta kiya akan tursasata ko ayi amfani da karfi ko kuma ta hanyar kayarda ita jarabawa da nufin samo kanta, ta kara da cewa akwai kulab na dalibai wanda suke hada baki da miyagun malamai da kuma manyan gari domin lalata rayuwar ‘ya ‘ya mata, wannan babban abin tashin hankali ne kwarai da gaske. Alokacin da nake sauraren wannan wasika wallahi saida na zubar da hawaye domin ganin irin halin da ‘yan uwanmu suke ciki a jami’o’i.

Akan wannan batu, ni ganau ne, domin naji labarin irin yadda ake dabdala acikin jami’o’I kuma na gani musamman da daddare. Abinciken da nayi na tabbatar da haka don Alhazan birni kanshiga jami’o’I da daddare su debo dalibai mata su je suyi fasikanci da su sannan su dawo da su kai wani abin tashin hankalima wasuma acikin mota suke aikata irin wannan ta’annati acikin jami’a kawai sai dai suyi nesa da idan jama’a wannan ba boyayyan abu bane a jami’a.

Idan muka koma kuma batun waccan wasika da wannan daliba ta aikowa da mallam, acikin wasikar tayi bayanin cewa tanada wanda take so kuma yana da sana’arsa dai-dai gwargwado tace taji ta gani ko agidan kara zai zauna da ita amma iyayanta suka ce sai ta gama jami’a sannan tayi “tsada” kamar yadda tace. Wannan babban kalubalene ga iyaye domin a kokarin da suke na ganin ‘ya ‘yansu sunyi karatu sun zama wasu kuma sun taimakawa rayuwarsu wajen fadawa cikin halaka. Domin babu wanda yake da garantin cewa ‘yarsa zata kamala jami’a bata fada cikin irin wancan tarkon ba. Tabbas rayuwar ‘yarka abin tambayace a gareka ranar gobe kiyama.

Kamar yadda na fada a baya da yawa dalibai kanyi dokin jami’a afarkon shiga kuma da tunanin cewa sai sun gama sun fara aiki sannan zasuyi aure, wannan takan sanya da yawa fadawa cikin hadari domin da yawa basa gane kuskurensu sai lokacin da suka gama jami’a suke naman mazajen aure kaga da yawan mutane na gudun wacce ta kamala jami’a kodai tsoron irin abin da waccan yarinya da ta fada cewa ya fada akanta ko kuma wani abin da ya ke ba wannan ba.

Kamar yadda ya rinyar ta nema da cewa don Allah malam acikin irin wannan mawuyacin hali da ta sami kanta, a irin wannan hali na fadawa tarkon shedan cewa shin idan tayi zina shin laifin nata ne ko na mahaifinta, a lokacin da mallam yazo wannan gabar sai da yayi ajiyar zuciya. Tayi maganganu masu daukar hankali tace ya kamata iya ye su tuna shin su a yadda suke ya sukeji a lokacin da sha’awa ta motsa musu, ballantana kuma ga ‘yan mata suna cikin shekaru kanana ga kuma motsuwar sha’awa a kowane lokaci kasan cewar suna cakuduwa da maza a koda yaushe, akwai abin tsoro ainun acikin wannan yanayi.

Anan nima zanyi amfani da wannan dama nayi kira ga iyaye cewa. Wallahi kowannenmu zai bada bayanin yadda ya gudanar da rauywarsa da kuma rayuwar wadan da take ta’allake da tasa wato ‘ya ‘yansa yana da kyau iyaye su sake tunani akan ‘ya ‘yansu musamman mata, da yawan basu cika neman shawarar ‘ya ‘yansu mata ba akan halinda suke ciki da kuma irin abin da suke bukata. Yana da kyau ka sami lokaci ka rika tattaunawa da ‘yarka kanajin shawararta akan halin da ta ke ciki tare kuma da jin me ta ke da bukata, domin mata kamar tangaran suke dole sai ana kulawa dasu lokaci zuwa lokaci, da yawa idan ka tuntubi iya ye mata da maza basu san ya rayuwar ‘ya ‘yansu ta ke ba musamman yadda suke gudanar da al’amura da suka hada da kuma halinda suke ciki dangane da karatunsu.

Akwai wani uba da na sani ‘yarsa tana jami’a amma baisan me ta ke karantawa ba kawai tsakaninsa da ita ya bata kudin makaranta wane hali take ciki babu abinda ya dameshi. Haka kuma ba kowane uba ne yake bibiyar cewa ya karatun ‘yarsa yake a semester kaza ba yarinya tayita samun carryover a karshe har ace sai ta maimaita shekarar amma agidansu babu wanda ya sani, ambarta ita zata yiwa kanta tunani kuma ita zata yankewa kanta hukuncin halinda da ta ke ciki.

Yana da kyau iyaye su dawo daga rakiyar wannan al’ada da take zagwanyar da tarbiyyar da aka dade ana tsuwurwurinta wajen ganin yara sun kasance na gari. Hakkin ka ne ka janyo ‘yarka ajiki kaji kokenta domin ganin yadda zaka maganta mata. Malamai suka gaya mana cewa “manzon Allah yakan zauna da diyarsa Fatima yaji halinda take ciki, haka kuma yakan je har gidanta ya zauna a tare da ita yana jin irin halin d suke ciki ita da mijinta” wannan babban abin koyi ne da iyaye zasu koya daga baban Fatima kakan Hassan da Hussaini salallahu alaihi wasallam. Allah ya shiryemu ya shiryi zurriyarmu.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@yahoo.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment