Sunday, July 24, 2016

Meye Ake Nufi Da Film Village?


MEYE AKE NUFIN DA FILM  VILLAGE? 

Wannan tambaya ce da dan uwa Malam Misbahu Saminu Madabo yayi a Shafin sa na Facebook. Sakamakon tattaunawar da naga ana yi a karkashin posting din nasa yasa na bashi amsa kamar haka:
Alkali Misbahu Saminu MadaboMadabo sannu da kokari. Daga wannan tambaya da kuma maganganun da masu koment ke yi ya nuna da dama kawai sunan suka sani amma sam basu fahimci meye ake nufi da film Village ba.

Amma a zance na hakika Film Village da Gwamnati zata gina, wani waje ne da zaka kirashi ma'aikata da za a tanadar masa abubuwan bukata irin na abinda aka yi domin sa.  Misali, idan Gwamnati ta gina Film Village zai zama tamkar garin aiki ne. Wato duk wanda zai shirya film zai je wannan waje ya biya Gwamnati kudin amfani da wajen sannan a bashi iznin shiga, wajen zai kunshi lambu da dakunan daukar hoto da wajen tace sauti ko Studio, da kuma nau'I na Kyamarori da suturu da abubuwan da masu film zasu bukata, za tanadar da komai, amma fa duk abinda mutum zai yi amfani zai zama sai an biya kafin fara amfani da shi.

Bayan haka kuma, Gwamnati fa ba wai kawai wajen zata gina ta dankawa masu shirya film sai yadda suka ga dama ba, ba haka bane, wajen zai kasance akwai jami'an tsaro da zasu dinga sanya ido akan masu shiga da fita, dan tabbatar ba sace ko lalata kayan da aka sanya dan amfanin wajen ba. Jami'an tsaro anan ba ina nufin zata zuba sojoji ko 'yan sanda ba, za a samarwa wajen Security ne da ya dace da kuma wanda aka ga yayi daidai.

Sannan kuma, a cikin wajen dai za a bayar da damar bude kantuna na sai da abinci da kayan ciye ciye. Wanda wannan gwamnati na da zabi ko dai kantuna su zama nata ma'ana abinda ake sayarwa ko kuma a baiwa mutane shaguna su kuma su zuba kaya a ciki.

Gwamnatoci na samar da irin wannan waje ne, dan kebe masu yin a abin da kuma samar masa da tsarin da zai bawa hukuma damar samun cikakken kudin shiga. Amma fa mutane su sani, duk wannan abinda za ai tilas Gwamnati zatai ne bisa la'akari da yanayi da kuma al'adunmu da suka dace da addini. 

Misali idan Gwamnati ta gina, zata ce dokokin jihar Kano sun haramta sha da sayar da giya. Dan haka zai zama doka a wannan waje ba za a sayar da giya ko shanta ba, dan haka wanda duk aka kama ya karya dokar shan giya ko sayar da ita a wajen zai fuskanci hukuncin da aka tanadar wa hakan. Wannan ya hada da sauran abubuwan da Musulunci ya hana, kuma dokokin Jihar Kano suka tabbatar da haninsu kamar Zina, Luwadi, Sata, Sane, kwace fada da sauransu.

Bugu da kari, akwai wajen shakatawa na Gwamnati dake Yankari a Bauchi, a wannan waje akwai dakunan kwana da wajen ganin na mun daji da kuma wajen linkaya. Kaga ai Gwamnati ce ta samar amma dokokin wajen sun dace da mutanan Bauchi da Arewacin Najeriya. Sannan kuma akwai irin wannan wajen shakatawa a Cross Rivers da ake kira Obudu, a wannan waje sha da sayar da giya ba laifi bane, sabida a jihar shan giya da sayar da ita ba laifi bane. Amma kuma abinda zamu gane shi ne dukkan su da wannan film Village Gwamnati tayi ne dan samun kudin shiga, ba wai dan kawai bukatun wasu tsiraru bane.

Bayan haka kuma, Gwamnati ba wai kawai zata zura ido ayi duk abinda aka ga dama ba, tilas akwai dokokin da za ai domin wajen. Dan ita Gwamnati zai zamar mata wajen samun kudin shiga. Tunda kasashe irinsu India da Turkiyya da Masar suna da irin wannan waje, kuma yana daga cikin abubuwan samar musu da kudin shiga.

A dan haka, mutane su sani, wannan waje zai zama ne kamar gidan tarihi na Arewa dake Kaduna. Gwamnati ce ta gina, amma ana zuwa a kama hanyar dakuna a kwana, sannan kuma akwai dakunan taro wanda za a biya a gudanar da wani sha'ani.

A Takaice wannan shi ne Film Village kuma shi ne abinda Gwamnati zata gina a Kano. Duk wanda yace ba haka bane, to bai fahimci meye Film Village ba. 

Dan gane da batun lalacewar tarbiyya kuwa. Duk wanda misali ya karbi wannan waje dan gudanar da wani sha'ani kuma ya karya doka to akwai tsari na hukunci. Sai dai kuma wanda zai yi ba a sani ba, amma wannan ba zai sanya a hukunta wajen da aikin wasu tsiraru ba tunda ba manufarsa batawa ba.

Kamar Musulmi ne yaje ya aikata ta'addanci yasa Bom ya kashe mutane. Wannan ba zai zama dalilin da zai sanya a hukunta Musulunci da cewar shi ya horar da shi wannan aikin ba. Duk kuwa da cewar wanda yasa Bom din ya kashe Mutane Musulmi ne. Dan haka, ba zaka hukunta Film da aikin da kaga wani yayi da bai dace ba. Allah shi ne mafi sani.

Yasir Ramadan Gwale 
24-07-2016

No comments:

Post a Comment