Thursday, July 21, 2016

Gaskiya Da Rikon Amana Da Aiki Tukuru Suka Janyowa Malam Nuhu Ribadu Martaba Da Daukaka


GASKIYA DA RIKON AMANA DA AIKI TUKURU SUKA JANYOWA MALAM NUHU RIBADU MARTABA DA DAUKAKA 

Malam Nuhu Ribadu mutum mai gaskiya kamar Littafi. Ka duba yadda gaskiya da rikon Amana da aiki tukuru suka janyowa Malam Nuhu Ribadu martaba da daukaka. A kakar zaben 2015 Malam Nuhu Ribadu ya shiga tsaka mai wuya, wadda ta janyo dukkan jam'iyyun APC da PDP suka yi ta kokarin ganin shi ne zai zamar musu dan takarar Gwamnan Jihar Adamawa. Cikin ikon Allah mai aukuwa ta auku, Allah ya kaddari Malam Nuhu da samun tikitin tsayawa takara karkashin jam'iyyar PDP. 

Yanzu kuma bayan dan wani lokaci jam'iyyar APC ta fahimci irin wawar asarar da ta yi ta Malam Nuhu Ribadu, dan haka suka yi ta aika masa da wasiku na fatan alheri da fatan ganin ya koma APC. Mu muna da masaniyar dukkan abubuwan da suka wakana wanda suka janyo ficewar irinsu Malam Nuhu Ribadu da Sardaunan Kano Malam Ibrahim Shekarau fi cewa daga APC jam'iyyar da suka kafa ta da hannunsu,  suka koma PDP. 

Malam Nuhu Ribadu na da damar zab'in abin da yaga yafi masa daidai kuma zai fi zama Maslaha a gareshi da al'ummarsa da kuma mu da muke tare da shi. Ni a nawa ra'ayin bana fatan Malam Nuhu Ribadu ya fita daga PDP ya tsallaka APC. Ina fatan ya cigaba da zama a PDP domin ko ina muna bukatar wakilcin mutane na gari. Amma idan ya yanke shawarar komawa APC wannan yayi hukunci ba wanda raina zai so ba, amma  ina masa fatan alheri. 

Na gamsu dari bisa dari akan nagartarsa da kishin sa da son sa da gaskiya. Allah ka taimake shi kayi riko da hannunsa, ka tabbatar da shi akan gaskiya komai rintsi.  

Yasir Ramadan Gwale 
21-07-2015

No comments:

Post a Comment