Sunday, February 22, 2015

Tsakanin Obasanjo Da Jonathan Waye Ba Mabarnaci Ba?

TSAKANIN OBASANJO DA JONATHAN WAYE BA MA'BARNACI BA?

Tsohon Shugaban Kasa ya zama Gwarzo a wajen Mutane da yawa masu saurin manta baya musamman a Arewa. Tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo mugun dan fashi ne kuma dan damfara, ya yiwa Miliyoyin al'ummar Najeriya fashin zabe a 2003 da 2007 da kuma hannunsa akaiwa al'umma fashi da damfara a 2011. Obasajo duk shi ne silar gurguincewar Demokaradiyyar Najeriya shi ya fara ginin tubalin lalacewar al'amura da yawa da suke cigaba da balbalcewa a yanzu.

Obasanjo shi ne yaci dunduniyar Arewa ta hanyar amfani da wasu rubabbun Gwamnoni na lokacinsa ya murgudewa cigaban Arewa kafa. Ya karya Babban Bankin Arewa da duk wani Dan Arewa ke alfahari da shi, sai da ya tabbatar yakai Bankin kasa ta yadda ba zai kara shurawa ba; Sannan Obasanjo ya yi amfani da karnukan farautarsa daga cikin Gwamnonin lokacinsa ya karya gidan Jaridar Arewa na NNN. Obasanjo ya lalata harkar Noma da kiwa a Arewa ya yiwa mutanan Arewa asara mai dumbin yawa da sunan wata cuta H1N1 da ake kira Murar Tsuntsaye, aka kashewa manyan Manoma dabbobi da tsuntsaye da sunan yaki da wannan cuta.

Bugu da kari Obasanjo ya karyar harkar Noma ta hanyar lalata Hadejia/Jama'are River Basin Development Authority. Ya shigo da wata irin ciyawa daga kasashen Turai wadda take tsotse ruwa tare da mayar da gulabe kufai, aka bi garuruwan da wannan kogi ya ratsa aka fesa wannan muguwar ciyawa duk da nufin karya manoma a Arewa ta yadda za ai shekara da shekaru mutanan Arewa basu farfado ba, wannan ya faru akan idan wadan da suka san abin. Ya lalata aikin Tafkin-Chadi yai amfani da sinadaran da suke busar da Tafkin duk domin karya tattalin arzikin Arewa. Obasanjo gawurtaccen Mabarnaci ne da ya yiwa Arewa zalinci na fitar hankali.

Sannan kuma, Obasajo ya shiraya wata kidayar jama'a ta bogi, duk domin gurgunata Arewa, aka i amfani da wannan kidaya ta karya aka rage mana yawan jama'a a Arewa, sannan aka karawa mutanan kudu yawa, Obasanjo yayi amfani da wannan kidaye wajen dankwafe Arewa, wasu jihohi a kudu da basu kai yawan jama'ar Gwale ba aka kambasu aka kara musu lamba duk dan a karyamu a nuna rashin yawanmu ko a kamantamu da mutanan kudu ta fuskar yawa. Bayan a bayyane take cewar yawanmu ya ninka ninkin ba-ninkim, domin a tsakanin mutanan Arewa ne kadai masu mata hudu da 'ya 'ya talatin ko arba'in suke da yawa bila'adadun.

A 2007 Obasanjo ne ya shirya zabe mai cike da kazanta wanda hatta turawa masu sanya Ido a zabe sai da suka yi Allah-wadai da wannan zabe. YarAdua da kansa da Obasanjo ya kawo shi sai da ya bayyanawa duniya cewar lallai zaben da ya kawo shi karagar mulki "kazantaccen zabe ne mai muni" ya kuma yi alkawarin gyara a harkar zabe a Najeriya, har ya kafa kwamatin Mai Shari'ah Uwai. Duk irin wannan fashi da Obasanjo ya yiwa 'Yan Najeriya bai taba yin Nadamarsa ba, bai taba neman gafarar 'yan Najeriya akan wannan mummnan ta'adi da ya tafka ba, bal ma bai taba ganin abinda yayi kuskure bane. Bayan kuwa a Arewa kowa yasan cewa Obasanjo ya zalinci mutane yayi mana fashi da damfara ta zabe.

Haka kurum rana tsaka, Obasanjo ya zama Gwarzo a idanun Mutane Arewa bayan bai taba nadamar dukka irin bala'i da musifa da ya tafkawa mutanan Arewa ba! ba shakka dukkan irin wata dangin barna da sakaci da shakulatun bangaro da Shugaban kasa mai ci Goodluck Jonathan ya tafka Obasanjo ne silar hakan, bai kuma taba shaidawa duniya nadamarsa ba akan haka, dan haka babu yadda Obasanjo zai zama gwarzon rana tsaka.

A ganina da Shugaban kasa Goodluck Jonathan da Obasanjo duk mabarnata ne, maha'inta da suka cuci Al'ummar Naijeriya sukai badakala mai yawan gaske, suka kasa sauke nauyin da ke kansu na shugabanci duk da irin ruwan-kudin da Allah ya yiwa gwamnatocinsa. Kudaden da Obasanjo da Jonathan suka samu sun isa a rushe Naijeriya a sake ginawa. Har yau Obasanjo bai bayyanawa duniya ina yakai kudin wutar Lantarki Dalar Amurka Biliyan Goma Sha-Shida ba, babu wutar kuma babu kudin. Haba, duk wannan almundahana da Obasanjo ya tafka akwai abinda zai aikata na rana tsaka da zai mantar da mu irin kitififin da ya shirya mana. Allah ka cece Najeriya daga hannun duk wasu miyagu azzalumai.

Yasir Ramadan Gwale
22-02-2015

No comments:

Post a Comment