Monday, July 30, 2012

Tsokaci Kan Azumi: Muhimmancin Lokaci a Watan Azumi #3



Tsokaci Kan Azumi: Muhimmancin Lokaci a Watan Azumi #3

Ya yan uwa barkanmu da sake saduwa a wannan lokaci mai dumbin falala na azumin watan Ramadan. Muna godiya ga Allah madaukakin sarki da ya nuna mana kashin farko cikin uku na wannan wata, Allah ya sa ibadun da muka gabatar a cikin wadan nan kwanaki goma da suka gabata karbabbu ne, Muna rokonsa tare da tawassali da sunayensa tsarkaka madaukaka ( Subahanahu wata'ala) ya sa ba kishirwar banza mukayi ba! ya Allah kaine kace mu roke ka zaka amsa mana, ya Allah mamallakin komai, muna rokon kayi mana rahama da iyayenmu da 'yan uwanmu da abokanmu baki daya, Allah ka amintar da mu a garuruwanmu, Allah ka bamu lafiya da zama lafiya a kasarmu baki daya, haka kuma 'yan uwanmu da suke cikin tsanani a kasar Siriya Allah ka kai musu dauki.

Ya 'yan uwa masu giram, kamar yadda muka sani yanzu Azumi kusan ya zama ba bako ba, zamu ce ya zama dan gari. Yanzu masallatai da guraren karatuttuka sun fara ja da baya, a farkon Azumi masha Allah, sai kaga dukkan guraren Ibada cike suke da jama'a amma kuma yanzu abin ya ja baya, da fatan 'yan uwana matasa zasu dage kada su karaya wajen Ibada.

Ya 'yan uwa masu girma, Ramadan wata makaranta ce, wadda ba wai kawai ta tsaya iyakar kwanakin Azumi ba, a'a ana son dukkan darasin da muka koya a Ramadan mu cigaba da dabbaqa shi har bayan azumi, shakka babu yana da kyau mu sani kuma mu sakankance, cewar dukkan wani wa'azi ko Nasiha da muka ji, tabbas ya zama hujja akanmu, don haka dole mu dage mu yaki shedan wajen aikata ayyukan da aka kwadaitar da mu, ya dan uwa, Ba lallai ba ne sai kazama Abdullahi Dan Abbas wajen sallah da karatun al-qur'ani da kiyamullaili ba, a'a ana son lallai mu ringa kwatanta irin darusan da muka koya a Ramadan, misali wani yana nan tun shekarar bara rabonsa da yin sallar Asubahi a cikin Jam'i amma yanzu alhamdulillah Ramadan ta sa yana fitowa sallah  tare da jama'a, to irin haka ake so mu dore ba kawai Idan Ramadan ya wuce ba shi kenan mun daina Sallah a jam'i mun daina ciyarwa mun dai sadaqa mun daina zakka mun daina taimako, lallai ne bayan wucewar Ramadan mu cigaba da dabbaka irin abubuwan da makarantar Ramadan ta koyar da mu, wannan shi ne yake nuna mana cewar lallaia mun amfana da lokacinmu a Ramadan.

Ya 'yana uwa, yana daga cikin abinda malamai suke gaya mana cewa idan kaga mutum ya dore da ibada a bayan watan Ramadan alama ce da ta ke nuna cewar lallai Allah ya karbi addu'o'insa da kuma ibadunsa, haka kuma yana daga cikin abinda yake nuna cewar ayyukan bawa iyakacinsu inda ya yi su, shi ne aga mutum ya koma mummunar rayuwar da yake yi kafin Ramadan kaga wannan ya nuna mana cewa wannan mutumin bai amfana da lokacinsa a cikin Ramadan ba, illa iyaka ya bata lokaci ya walar da kansa wajen yunwa da kishirwa, wannan babban abin tashin hankali ne kwarai da gaske ya 'yan uwa masu girma.

Yau ma anan zan dakata sai Allah ya kaimu wani makon domin dorawa a inda muka tsaya, muna rokon Allah ya shiryemu shiriya ta addinin musulunci, Allah ya sa ibadunmu karbabbu ne, marasa lafiyarmu gida da asibiti Allah ya basu lafiya, mu da muke da lafiya Allah ya karamana, 'yan kasuwarmu Allah ya sanya albarka a cikin kasuwanci, ma'aikata kuma Allah ya sanya albarka a cikin albashi, matan da suke neman mazaje nagari Allah ka basu, mazan da suke neman mataye na kwarai suma Allah ka basu, muna da dumbin matasa masu son aure tsakani da Allah amma babu yadda zasuyi muna fatan Allah ya hore mana gabaki daya.

Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com
www.facebook.com/yasirramadan.gwale

No comments:

Post a Comment