Saturday, July 14, 2012

Budaddiyar Wasika Zuwa Ga Shugaban Kiristocin Najeriya Pasto Ayo Oritsejafor

Budaddiyar Wasika Zuwa Ga Shugaban Kungiyar Kiristocin Najeriya Pasto Ayo Oritsejafor
Kamar yadda mai girma Pasto ya gabatar da takarda a gaban kwamitin kula da lafiya da ‘yancin dan Adam da ke kula da kasashen Afurka na majalisar dokokin kasar Amerika, Ya Pasto, ka gabatar da takarda mai taken Nigeria: west Africa’s Trouble Titan ranar 10 ga watan Yuli na wannan shekarar ta 2012. Kamar yadda ka yi bayani a gaban wannan kwamiti, ka yi bayani ne da sunan kiristocin Najeriya wadan da ka ke shugabanta, shakka babu daman babu wanda ya aikeka kayi bayani da yawun ‘yan Najeriya, don haka bamu yi mamakin irin salon da kabi ba wajen gabatar da wannan takarda ba, kuma daman babu wani musulmi da zai yi tsammanin zaka yi Magana da yawun musulmin Najeriya.
Na tabbata da Musulmi ne zai gabatar da wannan jawabi da kayi a gaban wannan kwamiti, to tabbas da zai yi bayanin asalin rikicin addini da samuwar Boko Haram a Najeriya, tundaga shekarar 1983 da aka fara samun rikicin addini a kudancin jihar Kaduna da rikicen rikicen zangon kataf da Tafawa Balewa a Jihar Bauchi da sauran fadace-fadace da suka faru kusan a mafiya yawa daga cikin jihohin Arewa kama daga Kaduna, Taraba, Adamawa, Bauchi, Gombe da kuma wanda yake faruwa yanzu haka kuma yaki ci yaki cinyewa na Jihar Plateau. Duk wannan al’amari da ya faru lokuta masu tsawo tarihi ya rike, kuma asalin rikicin addini a Najeriya babu inda musulmi suka taba takalar kirista da neman fitina.
Tunda muke a Najeriya babu inda aka taba rawaito cewar ga wani Musulmi ya zagi Annabi Isa ko Jesus ko kuma, ace ga Musulmi ya wulakanta littafin Linjila ko Baibul. Amma kiristocin da aka rawaito sun zagi manzon Allah ko sun wulakanta al-qurani a Najeriya bazasu lissafu ba.Ya mai girma pasto, ko kana da masaniyar daruruwan Musulmi da ‘yan sanda Najeriya wanda galibinsu kiristoci ne suka yiwa Musulmi kisan gilla a ciki da wajen Maiduguri da sunan farautar ‘yan Boko Haram a tsakanin watannin Yuni da Yuli na shekarar 2009, idan Pasto bai sani ba, kiristocin da yake jagoranata suka aikata wannan mummunan aikin ta’addanci, sannan kuma suka kashe shugaban Kungiyar ta Boko Haram wanda a tsarin Mulkin Najeriya aka kira da Extra Judicial Killing wanda wannan ta sanya mininstan Shari’a na wannan lokaci kuma Antoni Janar na shari’a na Najeriya Mista Micheal Kaase Aondoakaa ya tafi har kotun duniya ya bayar da hakuri akan cewa kisan da akayiwa shugaban kungiyar da kuke neman a sanyata cikin sahun kungiyoyin ‘yan ta’adda na duniya a matsayin cewa ankasheshi ba ta hanyar shar’ah ba, kuma yace wannan babban laifi ne da Najeriya take neman gafar kotun Duniya akansa.
Ya maigirma Pasto, ko kasan cewa jaridun Najeriya sun rawaito cewa kiristoci sun kashe sama da Musulmi 630 a kauyen Yalwa a karamar Hukumar Shandam a jihar Plateau a shekarar 2004, kuma suka yiwa dubban matan Musulmi fyade kafin su kashe su, baya ga kuma daruruwan yaran Musulmi da aka sace bayan ankashe iyayansu, aka maida su bayi a kasarsu ta haihuwa, wasu kuma aka yi musu zane a fusakarsu domin batar musu da kamanni, duk wannan ya faru a Najeriya kuma kiristocin da Oritsejafor ka ke jagoranta su suka aikata wannan ta’addanci. Bayan haka kuma masallatan Musulmi da kiristoci suka rusa su har kasa a jihar Plateau da Kaduna bazasu kirgu ba.
Sannan a shekarar da ta gabata kiristoci suka farwa Musulmi da harbi da sara da suka suna kisa babu ji babu gani a Jos yayin da Musulmi suka fito sallar idi, duk wannan kiristoci ne wadan da Oritsefor ka ke jagoranta suka aikata, wa kuka tuhuma da laifin aikata wannan harin na Ta’addanci?  Amma da ka gabatar da wannan takarda sai kayi Magana da sunan Kiristoci kawai, wannan bai bamu mamaki ba, kuma ba matsala bace. Kamar yadda ka ke fada a cikin takardar da ka gabatar kana cewa “ kiristoci suna bukatar ‘yanci a Najeriya, suna bukatar ‘yancin yin addini” to nima ina fada maka da babbar murya cewar Musulmi suna da bukatar ‘yanci kuma, suna bukatar ‘yancin yin addini kamar yadda dokar kasa ta baiwa kowa damar yin addinin da ya zaba.
Nayi mamakin irin yadda pasto ka ke cewar kiristoci suna bukatar ‘yancin yin addini a Najeriya. Shin akwai wanda ya hana kirista yin addininsa? shin shugaban kasar Najeriya ba kirista bane? Shin shugaban Majalisar Dattawa ba kirista bane? Shin wane irin ‘yancin addini ka ke kira ya kai wannan Pasto? A baiwa kiristoci dama su ringa kashe musulmi babu ji babu gani, su ringa fyade wa matan Musulmi ko kuwa su ringa sace ‘ya ‘yan Musulmi suna yi musu zane a fuska suna mayar da su kiristoci!
Idan mai girma Pasto ya koma baya ya kalli tarihi da kyau, zai ga cewar Turawan Mulkin Mallaka da suka shigo kasashen musulmi, shin ba yada addinin kirista suka zo yi ba? kuma suka kwashi bakaken fata da nufin kaisu kasashen turai domin suyi aikin Bauta. Ko Pasto ya manta da mutanan kasar Aborigines (Australia) kusan mutum Miliyan 20 da turawan Mulkin Mallaka suka mayar kiristoci, ko Pasto ya manta da Kusan mutum miliyan 150 daga cikin Indiyawan daji da aka mayar kiristoci ta karfi da yaji a kudanci da Arewacin Amerika(North and South America), duka wadan nan fa iya yan gidanka da ka ke neman tanyonsu da agajinsu suka aikata wannan da sunan addininka na Kirista.
Idan pasto ya sake komawa ba a tarihi, kusan Mutum miliyan 180 aka dauka daga cikin Musulmi da maguzawa a Arewacin Afurka da yammaci da gabashi da sunan aikin bauta kuma aka tilastamusu komawa addinin kirista ta karfi da yaji wanda bayanai suka tabbatar da cewar kusan kashi 80 yanka su akayi aka zuba a cikin tekun Atalantika, wannan ta sanya har sai da ruwan teku ya sauya launi zuwa launin jini daga nan aka samu Red Sea. Kashi 12 a cikin waccan lambar aka dauka zuwa turai domin aikin bauta bayan antilasta musu komawa kiristanci ta karfi da yaji.
Yakin duniya na farko da akayi a shakarar 1930 idan na tuna dai dai da kuma yakin duniya na biyu da akayi a shekarar 1945 duk su waye suka jagorance shi? Shin ba kiristocin da Oritsejafor yake neman agajinsu bane, kisan Yahudawa sama da miliyan shida (6m) da Hitler ya yi shin ba da sunan kiristanci ya aikata abinda ya aikata ba? Ya maigirma Pasto, kasar da ka ke ganin kamar itace ubangijinku, idan tace abu ya kasance zai kasance wato Amerika, ba it ace ta Harba Makaman Nukiliya masu guba ba ya yankin Hiroshima da Negasazki a kasar Japan? duk wannan ba aikin ta’addanci bane da kiristoci ‘yan uwanka suke aikatawa mutanan da bau san hawa ba basu san sauka ba? Kamar yadda ya zo a cikin littafin Mattew a sabon alkawari, idan aka mari kirista a kuncin dama to ya mika na hagun a sake mari, shin kiristoci kun gasgata wannan sura da ta yi wannan bayanin kuwa?
Ita dai wannan kasar Amerika da ka ke kiran da ta kawo muku agaji a Najeriya, shin ba sune suka aikata kisan kishayi a kasar Vietnam ba, suka yi amfani da makamai masu guba akan talakawa bayin Allah, wannan ya sanya har yanzu a irin wadan nan kasashe ake haifar yara masu larura tunta gubar da kakaninnsu suka shaka, take binsu har yanzu? Missoloni ba kirista bane musulmi nawa ya kashe a kasar Libiya da basu jiba ba su gani ba?
Ya kai wannan Pasto, shin su waye suke aikata kisan kiyashi ga Musulmin gabas ta tsakiya da Afghanistan? duk lokacin da sojan Amerika ya aikata kisan gilla wannan sai kuce kuskure ne, amma kuma duk lokacin da aka sami kuskure wani Musulmi ya maida martini wannan shi ne dan ta’adda a wajenku shin wannan shi ne abinda iyayanku suka karantar da ku ken an, ko kuwa kuna son ku nuna mana cewa wannan it ace koyarwar addinin kirista?.
Idan muka dawo gida Najeriya, shin Musulmi nawa ne suka gamu da ajalinsu akan hanyar zuwa Jos a hannun kiristoci ‘yan kabilar Berom a jihar Plateau? Ko duk wannan Pasto bai san da shi ba, haka kuma, Musulmi nawa ne suka rasu a hannun tsagerun kiristoci a hanyar Kaduna zuwa Abuja a dai-dai kauyen Gonin Gora? Ko wannan shima Pasto bashi da Labari, duk fa wadan nan kiristoci ne suke aikatawa.
Kuma ita wannan kungiya ta Boko Haram da Pasto ya nace sai ansanyata a sahun kungiyoyin ‘yan ta’adda na duniya, shin kiristoci kadai suke kaiwa hari? Bayanai sun tabbatar da cewar duk wanda aka kama da sunan Boko Haram idan banda Kabiru Sokoto duk kiristoci ne, da Lucy Dangana da aka kama da safarar Makamai a kan iyakar Adamawa da Kamaru da kiristocin da aka kama bila adadun da yunkurin tarwatsa coci-coci da nufin gogawa musulmi kashin kaji, a ina Pasto yake duk wadan nan abubuwa suke faruwa? Me kuma ya yi akan wadannan al’amura da suka faru?
Mutum nawa sojojin JTF wanda galibinsu kiristoci ne suka kashe da sunan farautar Boko Haram, a Yobe da Maiduguri da Kano, su shiga gidan mutane suyiwa matan musulmi Fyade a gaban ‘ya ‘yansu a gaban mazajensu, kuma sannan su kashe mazan bayan sun kamala aikata badala da iyalansu, duk fa wannan ba wani boyayyan al’amari bane. Kuma ita wannan kungiya ta BH mu muslmi muna zargin tana da alaka da ku kiristocin Najeriya, domin a baya rahotannin sun nuna cewa magabacinka Jerry Gana ya taba yin belin tsohon shugaban BH da aka taba kamawa, shin babu alaka tsakaninku da wannan kungiya? Idan babu rami me ya kawo batun rami, lallai biri ya yi kama da mutum!
Ya kai wannan Pasto, muna tabbatar maka cewa mu Musulmi wallahi ba matsorata bane, kuma bamu taba yin nadamar kasancewarmu Musulmi ba, duk da wuya da tsanani da tashin hankalin da muke gani, wannan babu abinda yake kara mana illa kaimi da kara samun nutsuwa akan wannan addini namu, mun shaida cewa Allah mahaliccinmu yana nan kuma yana kallon duk abinda ke faruwa, Mun shaida cewa Manzon Allah annabin Allah ne, kuma mun shaida cewa Lahira gaskiya ce, aljanna gaskiya ce, wutar jahannama gaskiya ce, Ya mai girma Pasto muna tabbatar maka da babban baki da wasali cewa mu musulmi bazamu taba zama karakshin inuwar kiristanci ba a Najeriya, zamu cigaba da kasancewa mutane masu ‘yancin yin addininsu a duk inda muka tsinci kanmu.
Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com
www.facebook.com/yasirramadan.gwale

No comments:

Post a Comment