Monday, March 5, 2012

Yunkurin Rage Yawan Musulmi a Najeriya ta Arewa!!!

A shekarar dubu biyu da shida (2006) da ta gabata tsohuwar gwamnatin shugaba cif Olushegun Obasanjo da ta shude ta gudanar da kidayar jama’a a Najeriya. A wannan kidaya da akayi kamar yadda aka bayar da rahoto ankirge ko kididdige adadin gidaje da kuma al’ummar Najeriya, inda aka samu alkaluma da suke nuna cewa Najeriya tana da yawan mutane da adadinsu yakai kusan sama da miliyan dari da sittin da biyar (M165) wanda wannan kidaya ta nuna cewa Arewacin Najeria inda galibin mazauna wannan yanki musulmi ne, shi ne yakin da yake da kaso mafi yawa na al’ummar Najeriya, inda jihar kano tayi fice da kusan dadain da ya haura sama da mutum miliyan tara (M9) a cewar wannan rahoto; wanda kuma jihar legas da ke zaman jiha mafi girma akudancin Najeriya tazo ta biyu da kwatankwacin wannan adadi na kano, sai dai hukumomin jihar sunyi farat inda sukace basu yarda da wannan kidayar ba domin suna ganin babu yadda za’ayi ace wata jiha tafisu yawa a duk fadin Najeriya, haka nan suma hukumomin wannan jihar suka fito da nasu alkaluman kidayar masu cin karo da juna da na gwamnatin tarayya.

Abin mamaki, kuma abin daure kai, har wayau kuma abintambaya, dangane da wannan kidaya shi ne me ya sa ba’a kirga adadi ko yawan al’ummar Musulmi da kirista ba a wannan kidaya. Lallai ya kamata duk mai hange ya yi wannan tambaya shin meyasa aka tsallake batun addini a wannan kidaya? Kasan cewar Najeriya kasa ce da addini yake da tasiri ainun tsakani Musulmi da kirista, kuma zai zama abu mai muhimmanci ta wajen sanin adadin Musulmi da kuma Kirista, domin ganin yadda ya kamata a rika rabon mukaman gwamnati tsakanin musulmi da kirista, amma gwamnatin Obasanjo ta wancan lokaci ta ki yarda da a kirga yawan Musulmi da Kirista; sai dai a bayyane ta ke cewar ko a kirga yawan musilmi ko kada ayi hakan, a bayyane take cewar musulmi sune suke da kaso mafi yawa acikin al’ummar Najeriya, wanda ya sani, ya sani wanda kuma bai sani ba ya sani; don ansan cewa mafiya yawan musulmi suna da matan aure fiye da daya kuma sunada yawan ‘ya ‘ya wannan ta sanya adadin al’ummar musulmi ke karuwa cikin sauri.

Kamar yadda bayanai suka nuna cewar Musulmai sune ke da kusan kason da ya haura sama da kashi 74.8 a cikin al’ummar yanki Arewa. Kamar yadda wannan kididdiga ta nuna yankin Arewa maso yamma(North West) shi ne yankin da yafi daukar kaso mafi yawa na al’ummar Arewa, kuma wannan yanki shi ne yake da kaso mafi karanci na al’ummar kirista, domin idan ka cire kudancin kaduna babu wani guri kuma da yake da kiristoci masu dan dama a wannan yanki. Sannan kuma idan ka dauki yankin Arewa maso gabas(North East) shi ne yankin da yafi na yamma yawan kiristoci, sanin kowa ne akwai kiristoci a jihoin Adamawa da Taraba da Bauchi da Gombe da kuma jihar Borno, kusan idan ka dauki wadan nan jihohi jihar Taraba itace jihar da ta fisu yawan kirista sannan Adamawa da Gombe da Bauchi da kuma Borno ke binta a baya. Daga nan sai yankin Arewa ta tsakiya(North Central) inda kididdiga ta nuna kamar ana kan-kan-kan tsakanin Musulmi da kirista; amma sai dai a zahirin gaskiya ba haka bane domin idan ka dauke jihohin Benuwai da Pilato sune kadai jihohin da kiristoci suke da rinjaye, idan kuma ka kalli jihohin Kwara da Kogi da Nassarawa da Niger kusan musulmi suke da rinjaye a wadan nan jihohi.

Tun lokaci mai tsawo kiristocin Arewa suke ta kokarin kara yawan al’ummar kirista a wannan yanki na Arewa ta hanyar shiga lungu da sako na yankunan wannan yanki domin su maida mutanan da basuyi imani ba wato maguzawa kiristoci, wannan kuma ya faru ne da gudunmawar Turawa ‘yan Mishan, tun kusan zamanin ‘yan mulkin mallaka; domin a lokacin da yarima mai jiran gadon sarautar Birtaniya Prince of wales yarima charles ya kawo ziyara jihar kano, yaje gurare daban-daban daga cikin guraran da ya ziyarta harda wani kauye da ake kira kadawa a yankin karamar hukumar Kura inda bayanai suka tabbatar da cewar wannan kauye a kusan shekaru 80 ko sama da haka da suka gabata wata baturiyar ingila ta taba gina coci a kauyen wannan ta sanya ya kai ziyara cikin baraguzan cocin domin ya tuna da aikin da tayi, inda aka daukeshi hotuna aciki, domin garin da yake a wancan lokacin yanzu ya tashi. Haka kuma, kiristoci sunayin dukkan mai yuwuwa wajen kama kudancin jihar Kano domin a wata ziyarar wa’azin maguzawa da na kai zuwa wasu yankunan kananan hukumomi dake kano kamarsu Sumaila da Rogo da Bebeji da Kiru da sauransu tuni kiristoci sukayi nisa wajen maida yan uwanmu masu magana da yare irin namu da kuma al’adu da dabi’u irin namu, sunyi kokarin ribace musamman matasa da dama a wasu kauyuka inda aka maidasu kiristoci, misali a wani kauye da ake kira Gidan kota dake karamar hukumar Sumaila kiristoci sun mamaye kauyen inda suka giggina musu coci-coci da dakunan shan magani(Dispenseries) da basu taimakon takin zamani da garman Noma da basu suturu sababbi masu dauke da kodai hoton da ake cewa Yesu(Isa almasihu) ne ko kuma hoton paparoma john poul na biyu, haka abin yake idan ka shiga wani kauye da ake kira Bari a karamar hukumar Roggo da Talatar Jiddo a Bebeji, duk wannan anayi ne akan idanun Sarakunanmu na gargajiya wadan da ke ikirarin musulnci. Yanzu kuma wani shiri da kiristoci suke yi shi ne na mallake wasu yankuna namu misali, sunyi ta kokarin kama tare da mallake kudancin kowace jiha a yankin Arewa, idan ka dauki kudancin Kaduna sunriga sun mamayeshi tare kuma da kokarin kakkabe musulmi daga wannan yanki, duk wanda ya kalli rikicin zangon kataf da zankowa tundaga 1980 har zuwa yau zai tabbatar da haka, haka kuma suna ikirarin mallakar Kudancin jihohin Adamawa da Bauchi da Borno da Gombe da Niger da Nassarawa da Kogi da Kwara da wani sashe na kudancin jihar kebbi.

Wata dabara da kiristocin Arewa suke yi ita ce, suna daukar matasa masu jini a jika na wadan can kauyuka da muka ambata suna kaisu kasashen kudu ana horar da su yadda zasu kirawo ‘yan uwansu zuwa addinin kirista da basu ‘yan kudaden da zasu baiwa wanda yayi taurin kai da kuma yiwa masu unguwanninsu hidima da baiwa matansu sarkokin gicciye, domin zaka ga da yawa daga cikin mata da yara kanana da sarkokin gicciye(kuros) amma zasu cemaka su ba kiristoci bane, sannan kamar yadda na fada a sama suna yin amfani da garmar noma da sayan injin nika su baiwa duk wanda ya zama kirista; domin zaka ga limamin musulmi bashi da ko keke hawa ga rigarsa duk ta yage amma ga wani daga zamansa kirista ya fara sanya sutura mai dan kyau da sabulan wanka mai kanshi da sauransu. Wanda kamar yadda na fada duk wannan yana faruwa ne akan idanunmu, munyi sake wasu sukazo har cikinmu suka dauki al’ummarmu suka mayar da su kiristoci munaji muna kallo, ba’anan gizo yake sakarba domin wadannan matasa da ake mayarwa kiristoci ana ta kokarin cusa musu akidar kin duk wani musulmi Bahaushe tare da nuna musu cewar mudin makiyansu ne, domin munyi watsi da su bama kulawa da su.

Tabbas, shirye shirye sun kankama na kokarin rage adadin yawan al’ummar musulmi a Arewa, domin idan muka kalli rikicin Jos da yaki ci yaki cinyewa, kullum Musulmi ake kaiwa hari a kashesu a lalata dukiyoyinsu duk wannan da manufa; da kuma rikicin kudancin Kaduna ka bincika yanzu mafiya yawan mazauna garin zankowa wadanda Hausawa ne musulmi yanzu sun bar garin inda suke samun mafaka a sansanin ‘yan gudun hijira dake mando a cikin garin Kaduna, kaga ke nan anacin nasarar kakkabe musulmi daga kudanci kaduna, duk wannan ‘yan bokonmu da sarakunanmu da tsofaffin sojoji da sababbin sojoji da ‘yan sandanmu da ‘yan siyasarmu duk suna kallo ana karar damu babu wanda zai iya magana, kwanakin baya mai martaba sarkin Katsina Abdulmumin Kabir yakai ziyara sansanin ‘yan gudun hijira a kaduna shakka babu wannan abin karfafa guiwa ne, ya kamata da majalisar sarakuna Arewa da kungiyar Jama’atu Nasrul Islam suyi wata hobbasa wajen ganin anmaida Hausawa mazauna garin zonkowa garinsu kuma anbiyasu diyyar rayukan da aka kashe musu tare kuma da biyansu diyyar dukiyoyinsu da suka yi hasara. Kamar yadda kungiyar CAN take ruwa tayi tsaki akn dukkan wani abu da ya shafi wani kirista.

Sannan hanya ta biyu ta kokarin rage al’ummar Musulmi shi ne amfani da akayi da kungiyar Boko Haram da kuma sunan musulmi. Shakka babu biri ya yi kama da mutum, domin wannan al’amari na Boko Haram yana kara bayyana cewa kwata-kwata ba Musulmi ne suke kai wadan nan hareharen ba; domin idan muka lura su wadan da suke kai harin nan da sunan wannan kungiya suna kaiwa jami’an tsaro ne, wannan wani hoto ne da ake nunawa na tsorata al’ummar musulmi daga shiga aikin dan sanda, sannan kuma a gefe guda ana yin amfani da ‘yansandan bogi da sojojin bogi suna kara kashe al’ummar musulmi da sunan farautar ‘yan Boko Haram, domin duk wanda ya kalli abinda rundunar hadin guiwa ta tsaro a jihar Borno ta JTF sukeyi ya kara tabbatar mana da haka, domin suna shiga gida-gida suna kashe mutanan da basu jiba basu gani ba, da sunan bankado ‘yan kungiyar Boko Haram; kaga kenan duka biyu ga hare-haren Boko Haram ga kuma kisan ‘yansanda da suke kashe fararen hula.

Tabbas yanzu ta bayyana cewa kiristoci musamman na Arewa sune suka assasa kungiyar Boko Haram tare da amfani da ita akan nuna cewa musulmi ne. Yanzu idan zamu iya tunawa ankama wata mata mai suna Lucy Dangana akwanakin baya a iyakar Najeriya da kasar chadi ta shigo da makami wadda wannan mata kirista ce ba musulma ba kuma ta nuna cewa wadan nan makamai na Boko Haramne, amma shiru ka ji batun, sannan ga shi Allah yana tonawa wasu da dama asiri inda ake kama kiristoci cikin kama irinta musulmi suna yunkurin dana ko tayar da Bom a coci da nufin cewa Musulmi ne kamar yadda ya faru a Yenagoa a jihar Bayelsa da kauyen miya barkate a jihar Bauchi, domin kafin Bom ya tashi a harabar coci saunawa ya tashi a tsakanin musulmi, musulmi nawa ne suka rasa rayukansu ta sanadiyar wannan rikici da ake ta dangan tashi da addini da Boko Haram, idan banda wadan nan ‘yan kwanaki da bayanai suke nuna cewa ana kai hari a harabar coci, ai kusan dukkan harin da aka kai musamman na baya-bayan nan na boma bomai a johohin Yobe da kano da Gombe duk musulmi ne da daman gaske suka rasa rayukansu.

Sannan daga karshe bayan duk wadan nan abubuwa da akeyiwa musulmi, sannan akoma ana bankawa dukiyoyinmu wuta tare da sanyawa mafiya yawancin kasuwanninmu wuta da nufin karya tattalin arzikinmu ta yadda za’a hanamu katabus, daman kuma ta ban garen karatun Boko anriga anyi mana fintinkau, abin da ake kira Quota system a gwamnatin tarayya duk gurin da ya kamata a sanya dan Arewa sai a sanya kirista daga Arewa, wanda kuma idan mukabi kididdiga ta ‘yan sanda da muke da su a Arewa zamu sha mamaki domin idan bamu zo kan-kan-kan da kiristoci ba ta kuwa bazamu tsere musu ba musamman a kana nan ‘yansanda da ake kira kurata, daman kuma su ake turawa kwantar da tarzoma, duk bayan wannan kitumurmura da kutungwila da makirci da aka shirya na murkushe al’ummar musulmin Arewa, gwamnatin tarayya ta gayyato sojojin kasar Amurka da sunan kokarin shawokan al’amuran tsaro, kamar yadda mukaji Sabon jakadan Amerika a Najeriya MacCulay yana fada bayan harin bom da aka kai akano cewa kasar Amerika tana tunanin bude karamin ofishin jakadancinta a Kano da kuma yadda zataga yadda zata taimakawa Najeriya wajen magance matsalolin tsaro, inda yace a shirye suke su horar da jami’an tsaronmu yadda ake iya kwance bama baman da aka dana kafin su tashi. Kaga duk wannan abubuwa ne da suke nuna biri yayi kama da mutum.

Lallai idan barci muke to yanzu lokaci yayi da al’ummar musulmi ya kamata su farka. Domin yanzu makircin da ake shirayamana yana ta kara bayyana, a yayin da duk wadan nan kutunguila da ake shirya mana take cin Nasara mu kuma muna can mun maida hankalinmu akan batun izala da darika ko batun maulidi bidi’ah ne ko ba bidi’ah bane, bayan ga babbar musibar da take tunkaromu da babu ruwanta da darika ko izala ko me maulidi ko marar maulidi, sannan wasu da suke ikirarin su musulmi ne har suna jawo wadan nan arnan a jiki suna nuna aiduk daya ake, wanda kowa yasan karya ne biyu muke, idan har munyarda mauludi musulunci ne ina kirista ina maulidi, me ya hada kifi da kaska, Bahaushe yace duk wanda baiyi sharar masallaci ba to tabbasa bazai kasa yin ta kasuwa ba.

Daga karshe ina addu’ar Allah ya tona asirin dukkan wadan da suke shiryawa mana wannan kullu kurciyar, kuma Allah ya maida kaidnsu garesu, Allah kaci gaba da yimana kariya da kariyar nan taka, kayi mana garkuwa da garkuwar nan taka, ka tsaremu ka taremana dukiyoyinmu, shugabanninmu na Musulmi kuma Allah ka shiryesu ka yi musu jagoranci, mu kuma Allah ka sanya mu kasance masu da’a da biyayya ga shugabanninmu.

Yasir Ramadan Gwale

Yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment