Friday, February 17, 2017

 
ALLAHU AKBAR: ALLAH YA JIKAN MALAM JA'AFAR ADAM!!!
 
Malaminmu Sheikh Jaafar Ibn Mahmud Ibn Adam (RH), shi ne mutum na farko daya fara fitowa k’arara yayi fito na fito da masu Da’awar cewa Boko Haramun ne, ashe bamu sani ba Malam ya fanshemu akan wannan jihadi da yayi na yakar wannan tunani. Watakila badan wancan yaki da Sheikh Jaafar yayi ba, da yanzu Ahlussunnah suna shan wahala wajen fayyace gaskiyar Magana cewa Ahlussunnah mun barranta daga wad’ancan 6atattu masu da’awar ce...wa karatun Boko da aikin Gwamnati Haramun ne.
 
Sai gashi duk wanda zai soki mabiya sunnah ko yayi mana gugar zana, ko ma kai tsaye ya alakanta mu da wad’ancan mutane, an yanke masa hanzari tuntuni. Domin duk girma da tarin Ilimin Falsafar mai falsafa, to Malaminmu Sheikh Jaafar Ibn Adam shi ne ya fara fitowa fili 6alo 6alo ya yaki cewa karatun Boko Haramun ne.
 
Saura da me? Mutum ne ya kasa kada kai da hujja, ya kasa zuwa da wujja wadda zata share abinda ka zo masa dashi na ilimi, dan haka ba shida wani abin yi, sai dai yace maka, ai tsanani ko kaifin kishin addini shi yake 6u66ugar da ‘yan ta’adda, har suna ikirarin ai masu irin wannan fikira sun samo ta ne daga Litattafan Ibn Taymiyya.
 
Mu kuma muka ce musu, zakewa a cikin ilimin Falsafa shi ne yake sabbaba barin Allah gaba daya. A garin nan Kano ba wani gari ba, akwai mutanan da muka sani sun daina Sallah sun daina Azumi sabida zakewarsu cikin mummunan tunani irin na Falsafa. Ko ba haka bane? Kuma abinda basu sani ba, munce ne duk inda Wahayi ya sauka babu batun yin aiki da hankali ko tunani.
 
Yasir Ramadan Gwale
17-02-2017

Monday, September 5, 2016

Hattara Da Abokan Facebook Da Baka San su Ba


HATTARA DA ABOKAN FACEBOOK DA BAKA SAN SU BA

Wani abu ya faru a wannan Makon da wani matashi a sanadiyar facebook. Yana da kyau mutane su dinga sanin hakikanin da su wa suke mu'amala a facebook kafin sakin jiki da mutum. Domin kuwa halin da ake ciki yanzu rashin aminci yayi yawa tsakanin wannan al'umma. 

Wani matashi mai suna Salman ya hadu da wani a facebook har ta kai su ga yin magana a Inbox. Suna tattaunawa da wannan mutumin mai suna Micheal amma ba ainihin sunansa Micheal din ya rubuta a facebook ba, ya sa wani suna daban. Suna hira har dai shi Micheal yake tambayar Salman cewar me yake yi na neman kudi a matsayinsa na matashi? Salman yace ba abinda yake yi. Anan ne shi Micheal ya yiwa Salman alkawarin samar masa aiki anan Kano.

Bayan haka, shi Micheal yasha daukar hoton office da gida da mota yana turawa shi Salman yana bashi labarin irin rayuwar da yake ciki ta jin dadi. Wannan ta sanya shi Salman nuna zilama da kwadayi akan abinda Micheal ke nuna masa. Anan ne suka sanya lokacin da shi Salman zai zo Kano tunda yana zaune ne a jihar Adamawa. Salman yazo bisa romon bakan da Michel yayi masa cewar zai sama masa aikin yi a kamfanin da yake aiki.

Ranar Juma'a sai Salman yayi niyyar zuwa Kano, dan haka ya kira Micheal ya sanar masa cewar gashi nan zai Taho.  Shi kuma ya amsa masa da cewar ba matsala Allah ya kawo shi lafiya. Da isowar Salman Kano da yamma ana dab da Magriba, sai ya kira Micheal yake gaya masa cewar gashi ya sauka a Kano. Anan ne shi kuma ya shaida masa cewar baya nan yana wajen aiki, amma zai sanya kan in yazo ya taho da shi zuwa masauki.

Salman na tsaye a tasha wajen karfe 7 na Yamma wani yazo ya same shi bayan da suka yi waya yayi masa kwatancen inda yake a tsaye. Yace masa shi kanin Micheal kuma yazo ne ya kaishi masauki, Salman ya bashi suna tafiya har cikin unguwar Sabon gari a Kano. A lokacin da suka shiga wani layi mara kwalta wanda kuma baya bullewa  (close) sai shi Salman ya lura wasu mutum hudu na biye da su a baya, da ya fahimci lallai wadannan matsa bin su suke yi sai ya tsorata. Yayi nufin ya dawo da baya ya gudu, sai sukai masa ishara da cewar zasu yanka shi idan ya gudu.

Suka nuna masa wani gida suka ce ya shiga, suna shiga gida suka nuna masa wani daki suka ce ya shiga. Ya dan tsaya gardama sai daya ya hankadashi cikin dakin. Bayan da suka tura shi ciki sukai masa mugun duka, suka kwace masa wayoyin sa guda uku, suka kwace masa Agogo da Zobe da kuma kudin sa. Sannan suka tambaye shi Katin cire kudi na ATM yace bai zo da shi ba. Suka caje kayan sa basu ga katin cire kudi ba.

Daga nan suka sanya shi ya tube kayan sa tsirara suka dinga daukar hoton sa, sannan suka ce masa, sai ya sayi wannan hoton Video da suka dauke shi ko kuma su yada video din a Whatsapp da Facebook. Suka ce sai ya saya dubu 70000. Ya amince zai basu kudin, a lokacin da yake yana hannunsu duk abinda suka ce masa baya musantawa. Da suka gama haka, wajen 8:30 na dare sai suka rako shi wai ya hau mota ya koma ya kawo musu kudin video din.

Suka fito da shi suka ce masa idan ya kuskura yayi magana ko yayi wani motsi zasu illata shi, haka ya basu hadin kai.  Suna tafiya da shi suna ce masa bi nan bi can, har dai da Salman yaga sun zo inda Jama'ah suke, kawai sai yayi ta maza ya rumbaci daya daga cikin su suka fadi kasa yana ihun Jama'a ku taimake ni b'arawo ne. Ganin haka sauran suka gudu shi kuma yaci Nasarar damke dayan katamau. Nan ne fa jama’a aka taru ana tambayar me ya faru. Da yake mutanan wajen kabilu ne suna magana da shi yaron da Turanci, sai suka nemi su bawa shi Salman rashin gaskiya. 

Nan ne fa, shi Salman yace wallahi ba zai sake shi ba sai an je wajen 'yan sanda. Suka yi juyin duniya ya cika shi, amma Salman yace sai dai a gaban 'yan sanda sannan zai cika shi. Haka kuwa aka yi, aka kira 'yan sanda suka tafi da su. Ana zuwa caji ofis Salman yayi bayanin abinda ya faru, aka ci Nasarar kama dukkan wadannan matasa a daren, aka tsare su. Da yake a lokacin wajen 11:30 sai 'yan sanda suka ce shi Salman yaje ya dawo da safe. Yace shi bai san kowa ba, suka ce masa ba wani wanda ya sani da zai iya zuwa ya tafi da shi.

Nan ne kawai shi Salman ya tuna cewar ya sanni. Kawai sai naji 'yan sanda sun buga min waya, suka bani labarin abinda ya faru dan haka suke rokon nazo na tafi da Salman. To nima a zahiri ban san Salman din ba sani na hakika, domin a facebook kawai muke gaisuwa, kuma ko a facebook maganar mu bata wuce gaisuwa. Amma da yake naje Adamawa da Azumi Salman yazo har inda nake ya gaishe ni. Anan ya karbi lambar wayata. 

Jin haka, na kira abokaina guda uku na basu labari nace su rakani wajen 'yan sandan. Bayan da muka je na gabatar da kaina a wajen 'yan sanda sannan aka sake yi min bayanin ainihin abinda ya faru. Suka ce na tafi da shi Salman na dawo da shi da safe. Na karbi Salman na kaishi ya kwana. Anan ne nake yi masa fad'a, nace wanne irin hauka ne zai sashi haka kurum ya dauki kafa yaje wajen mutanan da bai san su ba.

Sannan shi kuma yake ce min, ai shi yaudarar sa sukai, domin hoton da suke sakawa a facebook ba nasu bane, sannan sunan da suke amfani da shi shima ba ainihin sunansa bane. Sai daga baya ne ya gane wanda suke magana din ashe sunan sa Micheal. Alhamdulillah mun bi dukkan hanyoyin da suka kamata muka nemawa shi Salman hakkinsa. Kuma har ya koma gida. Dan haka, anan nake amfani da wannan damar wajen kira ga mutane lallai suyi taka tsantsan wajen sanin su waye zasu yi mu'amala da su. Ganganci babba baka san mutane ba, kawai su kira ka kuma ka dauki kafa kaje.

Bayan haka, kuma tilas mutane su rage kwadayi da son banza. Domin a garin kwadayin abin da mutum yake tunanin zai samu zai jefa rayuwarsa cikin garari. Don shi Salman wanda suka yi masa wannan abu zasu iya yin Kidnapping dinsa ko ma su kashe shi, ba abinda ba zai faru ba. Dan haka, mutane ayi hattara. 

Yasir Ramadan Gwale 
04-09-2016

Friday, September 2, 2016

Malam Salihu Sagir Takai Na Iya Zama Mafita A Siyasar Kano A 2019


MALAM SALIHU SAGIR TAKAI NA IYA ZAMA MAFITAR SIYASAR KANO 2019

Zaben Malam Salihu Sagir Takai a 2019 ka iya sanya jihar Kano ta kai bantenta. Malam Salihu bayan bukatar a tallata shi a gayawa al'umma waye shi, duk wani dan Siyasa a jihar Kano da me zabe da wanda ake zabe, babu wanda ke bukatar a sanar da shi Nagarta da Ingancin Malam Salihu Sagir Takai. Domin tuni bayanai suka kara be dukkan wani lungu da sako na jihar Kano suna bayyana kyawawan halayensa wanda ake fatan shugabanninmu su kasance. Malam Salihu na daya daga cikin tsirarun 'yan siyasa a jihar Kano da ya samu kyakkyawar shaida daga kusan Galibin b'angarorin siyasar Jihar Kano.

Maganganunsa da irin kalaman da yake furtawa sun nuna hakikanin irin zaton da ake masa na dattako da kamala da sanin ya kamata wajen jagorantar al'amuran al'umma. Tun Malam Salihu Sagir Takai yana Shugaban karamar hukuma ya samu Yabo da Shaida ta Alkhairi daga Jagoran Gwamnatin Lokacin Alh. Rabi'u Musa Kwankwaso. Duk da sun fito a mabambantan jam'iyyu wannan bata hana Kwankwaso yabawa halayen Malam Salihu a harkar Shugabanci da kiyaye dukiyar al'umma.

Wannan gaskiya tasa da ta bayyana ta sanya Gwamnatin mai girma Malam Ibrahim Shekarau tafiya da shi har kusan Shekaru takwas. Bugu da kari har yayi aikin sa ya gama a matsayin Kwamashina ba a same shi da wani abin Allah wadai wanda ya tabbata cewar yayi abubuwa na rashin gaskiya ba. Wannan ta sanya Malam Shekarau sanya shi a gaba domin zama magajinsa, amma bisa kaddarawarsa Subhanahu Wata'ala, bai kaddarawa Malam Salihu Sagir Takai zama Gwamnan Kano a lokacin da aka so ba.

Duk da rashin samun Nasarar da yayi, hakan bata sanya shi zautuwa ba irin ta gafalallaun 'yan siyasa da kan shiga muguwar damuwa idan sun fadi zabe. Dukkan kalaman sa suna cike da nuna mika lamura ga Allah da nuna cewar shi ne mai bayarwa ga wanda yaso a lokacin da ya so. Malam Salihu yaje kotu domin bin hakkin sa da yake ganin anyi ba daidai ba a zaben 2011 hakan bai nuna rashin tawakkalinsa ba, sai dai bisa tsari na rayuwa idan kana ganin an taka hakkin ka karbi kadu, wanda tsarin siyasar wannan lokaci yayi tanadin hakan.

Gwamnonin Kano da suka gabata Malam Ibrahim Shekarau da Alh. Rabi'u Musa Kwankwaso babu wanda bai bayyana kyawawan halayen Malam Salihu Sagir Takai ba. Haka nan,  shima Gwamna mai ci Alh. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana Malam Salihu Sagir Takai a matsayin mutumin kirki da ya dace da samun shugabanci. Ganduje tunda ya hau Gwamnan Kano bai taba yin wasu kalamai na batanci ga Malam Salihu sai dai yaba masa da yakan yi.

A dan haka, bisa wannan kyakkyawar shaida da Malam Salihu Sagir Takai ya samu, daga dukkan b'angarorin siyasar Kano da suka hada da Shekarau, Kwankwaso da kuma Ganduje ba suda wani sabani da Takai, kuma shima ba shida wani sabani da su a siyasance ko a mu'amala ta rayuwa. A sabida irin wannan kyakkyawan tunanin mu akansa muke ganin cewar shi ne mutumin da zai saita siyasar Kano, tare kawo sulhu da fahimtar juna tsakanin tsaffin Gwamnonin Kano. A duk cikinsu babu wanda yake da tunanin cewar Takai zai wulakanta shi ko tozarta shi, a sabida haka, muke fatan jam'iyyar PDP ta sake baiwa Malam Salihu Sagir Takai dama a 2019, sannan al'ummar jihar Kano su zabe shi domin saita jihar Kano da dora ta akan turba ta zaman lafiya da juna da fahimtar juna da kuma karuwar arziki da bunkasa jihar Kano tare da maida hankalin 2 aje ayyukan da zasu maida jihar Kano ta zarce tsara a Nigeria. 

Muna fatan Malam Salihu Sagir Takai a matsayin Gwamnan Kano a 2019. Idan har ka gamsu da wannan ra'ayin nawa ka bayyana goyon bayan ka ga ga Takai, ta hanyar rubuta, #Takai2019. 

Yasir Ramadan Gwale 
02-08-2016

Friday, August 26, 2016

Jakadan Sa'udiyya A Najeriya Ya Zubda Hawaye Don Tausayin Wata Mata


JAKADAN SA'UDIYYA A NAJERIYA YA ZUBDA HAWAYE DON TAUSAYIN WATA MATA

Mai Girma Jakadan Sa'udiyya a Najeriya, Sheikh Fahad Abdallah Sufyan, ya kadu matukar kaduwa sakamakon wani rahoto da ya karanta wanda Jaridar Daily Trust ta wallafa a ranar 13 ga watan Agusta 2016. Rahoton an yi masa taken, "Meet Kaduna Lady Who's Raising 5 Abandoned Babies" wato labarin wata mata da ta kula da rayuwar yara biyar tsintattu. Jakadan ya kadu ainun bayan karanta wannan Rahoto, inda ba da bata lokaci ya bukaci Ustaz Abubakr Siddeeq wanda shi ne Limamin Masallacin Abuja da yake Fassara huduba da Turanci, inda ya tambaye shi ko yaga rahoton da Jaridar ta buga. Inda Ustaz Siddeeq yace bai karanta ba. Nan da nan Jakadan ya turawa Ustaz Siddeeq hoton shafin jaridar da ya dauka a wayarsa ta Whatsapp dan ya duba ya gani. Jakadan ya kuma, bukaci Ustaz ya binciko  wannan mata tare da shirya masa yadda zai gana da ita ido da ido.

Labarin dai na wata mata ce mai suna Hajiya Uwani Yusuf Waziri, wadda aka fi sani da Uwar Marayu.  Wannan mata mazauniyar unguwar Kaji ce a jihar Kaduna. Tana da 'ya 'ya goma sha daya, duk da irin halin da take ciki, ta dauki gabarar kula da tarbiyyar yaran da aka tsinta ta rike su a matsayin 'ya 'yan ta. A duk lokacin da aka tsinci jariri a unguwannin Rigachukum ko Barakallahu ko Hayin Na Iya a kasan gada ko cikin Lambatu akan kai su gidan Hakimi, nan take shi kuma Hakimi zai tura da jairin da aka tsinta zuwa gidan Uwar Marayu. 

Ina cikin garin Kaduna a lokacin Jakada Sheikh Fahad Abdallah Sufyan ya bani wannan umarni.  Dan haka abin sai ya zo min da sauki wajen tuntubar yadda zan hadu da wannan mata. Dan haka ne na samu abokina Dr. Mahadi Shehu wanda shi ne Shugaban Kamfanin Dialogue Global Links tare da gudunmawar Maryam Ahamadu - Suka wadda ta hada wannan rahoto da tallafawar Rufa'at Maccido muka kai ga wanna mata.

Bayan da muka yi katarin gamuwa da Hajiya Uwar Marayu, muka sanya ranar Laraba 17 ga watan Agusta 2016, domin ganawar wannan mata da Jakada Sheikh Fahad Abdallah Sufyan da Misalin karfe 11 na safe a Birnin Tarayya Abuja. A lokacin Maryam da Hajiya Uwar Marayu sun zo tare da daya daga cikin marayun da wannan mata take raino mai suna Zainab, wadda take cikin zanin goyo. Mai Girma Jakadan Sa'udiyya Sheikh Fahad, ya yi mana tarba ta musamman a ofishinsa,  ya marabcemu da Shayin Larabawa na Gahwa da Dabino. A lokacin nayi kokarin zubawa kowa da kaina, amma Jakadan yace kar na damu zai zubawa kowa da kansa dan girmama Uwar Marayu. Bayan ya gama zubawa kowa Gahwa, ya kalli Zainab a cikin zanin goyo yace, yanzu wannan jariri bai yiwa kowa laifi ba na zuwan sa duniya amma an yasar da shi. 

A lokacin da Jakada Sheikh Fahad, yake bayani idanunsa sun cika da kwalla, zuciyarsa ta raurawa. Yayi ta kokarin yin magana amma ina kukan da yake a zuciya yaci karfinsa, inda ya kasa hadiye hawayen da suke kwaranya a kumatunsa. Ganin haka,  sai na Mikawa Jakada audugar share Gumi dake kusa da ni, dan ya goge hawayen da suke guda a kuncinsa. Dukkanmu da muke zaune a wannan waje, muka kasa jurewa, zukatanmu suka raurawa hawayen tausayi ya dinga bayyana a fuskokin mu, adaidai lokacin, Zainab dake cikin zanin goyo da bata san meke faruwa ba, ta fa she da kuka, abinda ya kara tsinka mana zukata, nan dai Uwar Marayu ta shayar da ita Madarar da ke tare da ita, wadda ke zube a cikin Bulumboti. 

Haka nan, Sheikh Fahad Abdallah, yayi karfin hali ya fara magana cikin murya mai cike da nuna tausayi da damuwa. Yace, masu Imani sune suke jibantar lamarin 'yan uwansu musamman wadan da suke cikin tsananin bukata. Kamar marayu da mata da aka mutu aka barsu da yara. Wadannan sune suka cancanci a taimaka musu. Ya k'ara da cewar, Manzon Allah Tsira Da Amincin Allah su k'ara Tabbata a gareshi ya ce, Ni da wanda yake jibantar al'amarin Marayu kamar yatsu ne guda biyu, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam yana mai nuni da yatsunsa biyu. Ya cigaba da bayani yana cewa; Watarana wani mutum yazo wajen Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam, yake ce masa, Ya Rasulullahi zuciya ta na fama da kunci da damuwa haka kurum, Manzo yace da shi, ka jibinci al'amarin Marayu ka ciyar da su daga abinda kake ci, Allah zai saukaka maka lamarinka, zuciyarka zata samu nutsuwa. 

Jakada Sheikh Fahad, ya cigaba da cewa, Hajiya Uwar Marayu kin cancanci jinjina da Yabo,  kuma kin cancanci ayi koyi da ke, kin zama zak'ak'ura a cikin matan Najeriya. Ya cigaba da bayanin cewar, duk wanda ya yayewa wani damuwa,  Allah zai yaye masa damuwa ranar tashin Alkiyama. Ke uwar marayu ce, ina tunasar dake Hadisin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam da yake cewa zamu shiga Aljannah tare da shi, yayi mata nuni da yatsunsa biyu; duk wanda ya jibanci al'amarin Marayu. 

Bayan da ya gama gajeriyar tunasarwa. Ya mikawa Hajiya Uwani Uwar Marayu wata gagarumar kyautar da ya bukaci kada a bayyanawa duniya kyautar da yayi mata. Sannan ya yiwa Marayun da take raino Goma ta Arziki. A hakikanin gaskiya zan iya cewa wannan kyauta da yayi musu Takai ta kawo duk da ya roki Alfarmar kada na bayyana abinda ya bayar, amma ya yiwa Uwar Marayu kyauta mai girma. "Wanda duk ya taimaki wani, shima Allah zai taimake shi ya jibanci lamarinsa."

Wannan abinda Jakadan Sa'udiyya ya yiwa wannan mata Hajiya Uwani Uwar Marayu ya kamata ya zabarurar da al'ummar mu wajen tausayawa Marayu musamman jariran da ake haifa kuma a yasar da su akan titi ko cikin Lambatu. Mu yawaita kyauta da sadaka domin bamu san Me Allah ya yi mana tanadi na alheri ba. Allah Ta'ala ya fada a cikin Sura Ta Biyu Aya Ta 268, Shaid'an yana tsoratar da ku da talauci da fatara, yana kuma yi muku bushara da rayuwa mai tsawo. Allah kuma yayi muku alkawarin Rahama da sakamako mai gwabi. Allah shi ne Masani mai hikima".

Hanzari: Wannan bayani Ustaz Abubakr Siddeeq ne yayi a shafinsa na Facebook da Blogspot. Ni kuma na fassara shi zuwa Hausa. Allah yasa mu dace.

Yasir Ramadan Gwale 
26-08-2016

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari


SHUGABAN KASA MUHAMMADU BUHARI 

Muhammadu Buhari Shugaban kasa ne kuma Shugaban mu ne, muna so masa Alkhairi kamar yadda muke so wa kanmu. Bama fatan Allah ya azabtar da shi a dalilin hidima da ya yiwa wannan kasa, muna fatan Allah ya sauka ka masa lamura ya bashi lafiya da ikon sauke nauyin da yake kansa. Bama aibata shi ko yi wasa mummunan fata, ko samun sakamako mai muni a karshen Gwamnatinsa, a ko da yaushe fatanmu shi ne, Allah ya saukaka masa lamura, ya aiwatar da ayyukan alkhairi ga wannan kasa tamu. Samun Nasarar sa shi ne cigaban mu, idan yayi Nasara kasarmu ce ta cigaba, idan kasarmu ta cigaba mune muka cigaba.

Bamu gushe ba, muna masa uzuri muna masa kyakkyawar fata. A kullum burin duk wani dan kasa na gari ne a ce kasar mu Nigeria ta samu cigaba fiye da dukkan kasashen Afurka. Ba muda wata kasa da za mu yi alfahari da ita da ta wuce Nigeria, dan haka duk wanda yake rike da ragamar jagorancin ta tilas ai masa biyayya da fatan ya samu Nasara wajen cimma manufofin sa na Alkhairi da yayi nufin wanzar da su a tsakanin wannan al'umma tamu.

Muna da masaniyar cewar babu wani shugaba da yake da hankali da kuma yasan me yake, da zai yiwa al'ummar sa mugunta da yi musu fatan shiga mawuyacin halin ni 'ya su. Kullum Shugabanni na gari buri suke da fatan saukakawa al'umma da kawo musu cigaba mai dorewa. Muna da masaniyar halin da tattalin arzikin kasarmu ya shiga na koma baya, wanda muke fatan ya zama Rahama a gare mu nan ga. Muna kuma fatan shugabanni na yanzu da masu zuwa nan gaba su himmatu wajen Alkinta dukiyar kasa domin amfanin jama'a. 

Amma duk da wannan buri da fata da muke yiwa Shugaban kasa, tilas ne mu fito mu nuna damuwar mu akan irin wannan mawuyacin hali da muke ciki. Ba laifi bane, dan wasu ko wani yayi korafin halin da yake ciki na tsanani, dukkan dan kasa yana da 'yanci daidai da kowa wajen bayyana gamsuwa ko rashin ta kan kowace irin Gwamnati. A dan haka muke kira ga Shugaban Kasarmu da yayi duba na tsanaki akan irin mawuyacin halin da al'umma suke ciki, a aiwatar da sauye sauyen da zasu kawo sauki a rayuwar al'umma ba tare da tsanantawa ba.

Hakkin Gwamnati ne kare muradun kasa da na al'umma. Amma kula da Al'umma shi ne akan gaba. Mutane suna cikin hali na yunwa, Masallatai da Majwmi'u sun zama tamkar wajen bara da roko, haka duk wata matattara ta jama'a, ta zama wajen roko. Mutane a cikin galabaita suke rokon abinda zasu ci dan su samu rayuwa. Khalifan Musulunci na biyu Umar Bin Khaddab Allah ya kara yadda a gare shi, yakan zama cikin zullumi da damuwa, akan kada Akuya tayi tuntube ko ta rasa abinda zata ci karkashin jagorancin sa Allah ya tambaye shi. Akuya fa tsoro yake kada Allah ya tambaye shi hakkin ta, sabida tsananin tsoron Allah.

Misalin irin zullumin da Umar Bin Khaddab ya kamata shugabannin su dinga kasancewa, domin samun kubuta a ranar gobe kiyama. Yanzu kai kadai a gidan ka, a tara maka iyalanka su yi maka tambaya akan hakkin su, sai ka shiga cikin tashin hankali da damuwa dan baka san me zasu ce ba. To ina ga tambayar ranar Alkiyama ace al'ummar Nigeria na batun hakkin su kan Shugabanni?  Ya kamata Shugaban kasa Muhammadu Buhari yaji tsoron Allah wajen tafiyar da Gwamnatinsa. A saukakawa al'umma mawuyacin hali. Allah ya bamu dacewa.

Yasir Ramadan Gwale 
26-08-2016

Thursday, August 25, 2016

Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sunusi Na Biyu Ya Tsage Gaskiya Akan Gwamnatin Buhari


SHIGA LAFIYA ALFANDA: MAI MARTABA SARKI MUHAMMADU SUNUSI II YA TSAGE TA

Ba shakka Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sunusi Na Biyu ya tsage gaskiya mai mugun daci  game da kudurorin wannan Gwamnati kan batun tattalin arzikin Kasa. Lokaci yayi da wannan Gwamnati zata bi shawarwarin kwararru domin ceto tattalin arzikin kasarmu daga halin tangal tangal din da yake. Idan ba haka ba kuma, labarai marasa dadi ne zasu ci gaba da faruwa. Abin kam akwai ban tsoro matuka idan aka cigaba da tafiya a haka. 

Ga kadan daga abinda mai martaba Sarki yace,  "misali a lokacin da Babban Bankin kasa CBN yake sayar da Dollar akan farashin hukuma na 197 amma mutane na saya 300 a kasuwar bayan fage, idan na zauna a gidana na dauki sailula ta ina da adadin mutanan da zan kira da zasu samo min zunzurutun kudi har Dollar Miliyan Goma a farashin hukuma na 197 ni kuma na sayar a farashin kasuwar bayan fage na 300, kunga kenan zan ci kazamar riba a wannan harka, domin na samu riba sama da Naira Biliyan Daya. Haka na nuna cewar idan na samu Dollar Miliyan goma sau hudu na ci ribar sama da Naira Biliyan hudu, Bugu da kari zan yi haka ne fa ina dakina ba tare da naje ko ina ba.

To a irin wannan yanayi ne fa ake cewar an shirya tattalin arzikin Ć™asa domin ya amfani talaka. Ku gaya min ta ina Talaka yake amfana, idan ba masu kudi bane suke sake kudancewa? Ya zama tilas Gwamnati tayi abinda ya dace domin ceto tattalin arziki daga lalacewa. Idan ba haka ba kuwa, Talaka zai sake shiga matsanancin talauci masu arziki kuma na kara kudancewa." 

Wadannan sune kadan daga cikin kalaman Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sunusi wanda Galibin jaridun yau suka wallafa. Don haka ya zama tilas Gwamnati tabi shawarar kwararru domin fitar da kasar nan daga halin da take ciki.

Allah ya taimaki Sarki ya kara masa lafiya da karfin fadar gaskiya komai dacinta. 

Yasir Ramadan Gwale 
25-08-2016

Tuesday, July 26, 2016

Zamani Riga


ZAMANI RIGA 

A lokacin Gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau, Gwamnati ta kuduri aniyar gina katafaren Hotel a Lamba One Ibrahim Taiwo Road, inda yanzu aka mayar makarantar Sakandare. Gwamnati tayi la'akari da yanayin Jihar Kano a matsayin ta na cibiyar Kasuwanci a Arewacin Najeriya dama Yammacin Afurka da kasashen dake kudu da Sahara, amma duk da wannan bunkasa da buwayar da Kano tayi a harkar kasuwancin saye da sayarwa, Kano din babu masauki wadatattu domin saukar baki. Wannan na daya daga dalilin da Gwamnatin Kano ta bayar a wani tsari da suka yi da aka kira Kano Economic Road Map.

Anyi wannan kuduri ne da kyakkyawar niyya dan habakar kasuwancin Kano. Kasancewar gari kamar Kano babu wani katafaren Hotel dan saukar baki irin na Alfarma. Dan haka ne aka sanya wannan damba ta samar da Five Star Hotel Lamba one Ibrahim Taiwo Road. Amma sai wannan abin ya samu mummunar fahimta daga kungiyoyin al'umma da wasu daga cikin shugabannin al'umma a jihar Kano. Inda aka dinga sukar lamirin gina wannan hotel, ana cewa Gwamnati zata gina wajen badala a kusa da cikin birnin Kano.

A haka wasu mutane suka je fadar mai martaba Sarkin Kano Marigayi Alh.  Ado Bayero suka gaya masa karya da gaskiya akan wannan yunkuri na Gwamnati. Daga ciki dalilin a da suka baiwa Sarki Allah ya jikansa, har da cewar wai za'a gina Hotel mai tsawo da baki zasu dinga zuwa suna gane sirrin Kano. Da wasu zantuka marasa tushenmu masu kama da abin dariya. A haka suka gamsar da Sarki Marigayi, dan haka ya ja Hankalin Gwamnati karkashin Malam Ibrahim Shekarau da ta jingina wannan shiri na samar da wannan hotel.

Meye Hotel? Hotel fa ba wani abu bane illa masauki. Kuma akan haka ake gina dukkan wani Hotel, masauki ne domin amfanin baki da zasu shigo su yi wani uzuri, ko kuma samar da wajen yin taruka da sauransu. Amma sai muka yiwa Hotel guguwar Fahimta. Wasu da dama da an ambaci Hotel kawai sai suce wajen fasikanci ne da aikata badala. Hotel masauki ne da mutum zai biya kudi ya kwana. Wanda duk ya kama ya aikata fasadi ko barna ba zai zama adalci a hukunta Hotel da aikin da wani yayi a cikinsa ba.

Yanzu a jiha Kamar Kano, idan ka cire Hotel din Tahir Guest Palace babu wani Hotel da yake biye da shi a daraja. Sauran duk basu wuce alallaba ba. Wannan mutum fa me Tahir ba dan kasarnan bane, amma mu kalli irin mahaukatan kudin da yake samu a Harkar Hotel. Shin yaushe ne zamu yi kishin kanmu wajen bunkasa tattalin arzikin kasarmu da jihar mu? Duk wanda yake matafiyi yasan muhimmancin Hotel, amma duk da haka muna yiwa Hotel Kallon wajen aikata fasadi da barna.

A irin haka muke yiwa komai fassara. Yana da kyau al'ummarmu mu fadada tunani, mu wanke zuciyar mu ta hanyar duba duk wani abu na zamani da yake da Maslaha a rayuwar yau da gobe. Amma kuskure ne mu dinga kafewa akan abinda ba muda cikakkiyar fahimta akansa. Allah ya sakawa Malaminmu Sheikh Dr. Sani Umar Rijiyar Lemo da alheri, domin a lokacin da ya bayar da fatawa akan daukar hoto ba laifi bane, na san wasu da dama da suka kafa akan Hoto Haramun ne suka sauka daga kan wannan ra'ayin.

Lallai wannan gari namu mai albarka da muke fatan Allah ya tsare mana shi ya yaukaka arzikin sa,  yana bukatar Malamai masu zurfin Ilimi irinsu Dr. Sani da Dr. Bashir da zasu dinga haskawa al'umma abubuwa musamman wadan da zamani yazo da su kuma ake da gajeran tunani akansu, domin shi zamani riga ne, idan yazo dauka ake a saka ba mayar da kai baya ba. Allah ka haskaka zukatanmu wajen karbar gaskiya da kuma aiki da ita.

Yasir Ramadan Gwale 
26-07-2016