Friday, September 2, 2016

Malam Salihu Sagir Takai Na Iya Zama Mafita A Siyasar Kano A 2019


MALAM SALIHU SAGIR TAKAI NA IYA ZAMA MAFITAR SIYASAR KANO 2019

Zaben Malam Salihu Sagir Takai a 2019 ka iya sanya jihar Kano ta kai bantenta. Malam Salihu bayan bukatar a tallata shi a gayawa al'umma waye shi, duk wani dan Siyasa a jihar Kano da me zabe da wanda ake zabe, babu wanda ke bukatar a sanar da shi Nagarta da Ingancin Malam Salihu Sagir Takai. Domin tuni bayanai suka kara be dukkan wani lungu da sako na jihar Kano suna bayyana kyawawan halayensa wanda ake fatan shugabanninmu su kasance. Malam Salihu na daya daga cikin tsirarun 'yan siyasa a jihar Kano da ya samu kyakkyawar shaida daga kusan Galibin b'angarorin siyasar Jihar Kano.

Maganganunsa da irin kalaman da yake furtawa sun nuna hakikanin irin zaton da ake masa na dattako da kamala da sanin ya kamata wajen jagorantar al'amuran al'umma. Tun Malam Salihu Sagir Takai yana Shugaban karamar hukuma ya samu Yabo da Shaida ta Alkhairi daga Jagoran Gwamnatin Lokacin Alh. Rabi'u Musa Kwankwaso. Duk da sun fito a mabambantan jam'iyyu wannan bata hana Kwankwaso yabawa halayen Malam Salihu a harkar Shugabanci da kiyaye dukiyar al'umma.

Wannan gaskiya tasa da ta bayyana ta sanya Gwamnatin mai girma Malam Ibrahim Shekarau tafiya da shi har kusan Shekaru takwas. Bugu da kari har yayi aikin sa ya gama a matsayin Kwamashina ba a same shi da wani abin Allah wadai wanda ya tabbata cewar yayi abubuwa na rashin gaskiya ba. Wannan ta sanya Malam Shekarau sanya shi a gaba domin zama magajinsa, amma bisa kaddarawarsa Subhanahu Wata'ala, bai kaddarawa Malam Salihu Sagir Takai zama Gwamnan Kano a lokacin da aka so ba.

Duk da rashin samun Nasarar da yayi, hakan bata sanya shi zautuwa ba irin ta gafalallaun 'yan siyasa da kan shiga muguwar damuwa idan sun fadi zabe. Dukkan kalaman sa suna cike da nuna mika lamura ga Allah da nuna cewar shi ne mai bayarwa ga wanda yaso a lokacin da ya so. Malam Salihu yaje kotu domin bin hakkin sa da yake ganin anyi ba daidai ba a zaben 2011 hakan bai nuna rashin tawakkalinsa ba, sai dai bisa tsari na rayuwa idan kana ganin an taka hakkin ka karbi kadu, wanda tsarin siyasar wannan lokaci yayi tanadin hakan.

Gwamnonin Kano da suka gabata Malam Ibrahim Shekarau da Alh. Rabi'u Musa Kwankwaso babu wanda bai bayyana kyawawan halayen Malam Salihu Sagir Takai ba. Haka nan,  shima Gwamna mai ci Alh. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana Malam Salihu Sagir Takai a matsayin mutumin kirki da ya dace da samun shugabanci. Ganduje tunda ya hau Gwamnan Kano bai taba yin wasu kalamai na batanci ga Malam Salihu sai dai yaba masa da yakan yi.

A dan haka, bisa wannan kyakkyawar shaida da Malam Salihu Sagir Takai ya samu, daga dukkan b'angarorin siyasar Kano da suka hada da Shekarau, Kwankwaso da kuma Ganduje ba suda wani sabani da Takai, kuma shima ba shida wani sabani da su a siyasance ko a mu'amala ta rayuwa. A sabida irin wannan kyakkyawan tunanin mu akansa muke ganin cewar shi ne mutumin da zai saita siyasar Kano, tare kawo sulhu da fahimtar juna tsakanin tsaffin Gwamnonin Kano. A duk cikinsu babu wanda yake da tunanin cewar Takai zai wulakanta shi ko tozarta shi, a sabida haka, muke fatan jam'iyyar PDP ta sake baiwa Malam Salihu Sagir Takai dama a 2019, sannan al'ummar jihar Kano su zabe shi domin saita jihar Kano da dora ta akan turba ta zaman lafiya da juna da fahimtar juna da kuma karuwar arziki da bunkasa jihar Kano tare da maida hankalin 2 aje ayyukan da zasu maida jihar Kano ta zarce tsara a Nigeria. 

Muna fatan Malam Salihu Sagir Takai a matsayin Gwamnan Kano a 2019. Idan har ka gamsu da wannan ra'ayin nawa ka bayyana goyon bayan ka ga ga Takai, ta hanyar rubuta, #Takai2019. 

Yasir Ramadan Gwale 
02-08-2016

No comments:

Post a Comment