Thursday, June 30, 2016

Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari A Yau


GWAMNATIN SHUGABAN KASA MUHAMMADU BUHARI A YAU 

Wani lokaci kan da ya shude bayan da wannan Gwamnati ta gama tattabata a matsayin na cikakkiyar Gwamnati. Naji wani mai kira yana kira da kakkarfar muryar yana ta b'urari yana mai Yabo da jinjina akan abinda akai yayi masa dadi na wasu da ake kamawa da ake zargin sun zambaci wannan kasa a zamanin Gwamnatin tsohon Shugaban kasa Dr. Goodluck Jonathan da ta shude, a lokacin da ake tsaka da wannan kame da daurin a gefe guda kuma farashin kudin musanye na hauhawa a kasuwannin canji. Anan ne naji wannan mai kira yana cewar su ba suda wata damuwa, Dollar Amurka daka fi amfani da ita a kudin musanye ta tashi ta kai Naira dubu su kam bukatar su ta biya, babu ruwansu da wani abu tashin dollar. 

Ba mamaki wannan mai kira a lokacin da yake wancan batu na Dollar tayi ta tashin gwauron zabi tana kanshin tura re dan goma a kasuwar musanye, bai san hakikanin yadda hauhawar farashin dollar yake shafar tsarin tattalin arziki ba, shi sa a zaton sa Dollar zata yi ta tashi shi kuma rayuwarsa ta cigaba da gudana yadda yake so. Kwatsam bayan wani lokaci sai na sake jin wannan me kira yana korafi yana fadin rayuwa ta tsananta ya kamata Gwamnatin da suka zaba ta yi wani abu akan halin da ake ciki na tattalin arziki da kusan farashin komai ya linka sakamakon tashin dollar da wancan mai kira yayi ta mata fatan tashi babu kakkautawa. 

Na saurari wani bayani na wani fitaccen Malamin masanin kimiyya da hamayya dan Adam, yana fadin cewar. Idan mutum yayi burin auren mace kakkyawa to ya tabbata ya same ta kuma ya aura,  haka nan kuma, idan ya aureta kada daga baya yayi korafin ba tada tarbiyya ko bata iya girki ba, domin asali ba hakan ya nema ba, kyau yake so kuma ya samu. Kamar me wancan kira ne akan wannan gwamnati, asali shi ne, yaso kuma yayi fatan Muhammadu Buhari ya zama Shugaban kasa kuma ya zama, to ba shakka shi bukatar sa ta biya tunda abinda yayi ta fata kenan.

Mafiya yawancin mutane sun so zuwan wannan gwamnati ne kai tsaye ba wai ainihin saukin lamari ake nema a wajen Allah ba. Misali a baya kafin zabe yana zama laifi babba akan wasu suyi addu'ah suce Allah yayi mana zabi mafi alheri, kawai an tafi akancewar tilas kowa ya goyi bayan Buhari watakila sabida k'abilanci da kuma Addini. Allah Buwayi ne gagara Misali,  a tsarin Mulkin Dimokaradiyya da babu ruwansa da addini, mulki ne da ke tafiya da manufofin jam'iyyun siyasa da kuma wanda aka zaba. 

A dan haka, akan samu wasu shugabannin suyi Gwamnatin adalci a tsarin Demokaradiyya sama da gwamnatin da ba ita ba da ta fi kusa da addini. Misali tsarin Gwamnatocin kasashen turai da Amurka ya sha bamban wajen tafiyar da gaskiya akan mafi yawancin tsarin mulkin da ba shi ba, a gani na zahiri sai kaga wadannan kasashen da suka cigaba suna kwatanta adalci a tsakanin Al'ummar da suke shugabanta. Sabbin sauran da ba su ba.

A dan haka game da Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ina ganin da yawa kawai fatan su zuwa ta ba wai sun kyautata zato ne ga Allah ba, illa shi wanda sukai masa fatan zuwa suke marari zai yi abinda suke so. To a ganina duk mutumin da yayi fatan zuwan wannan gwamnati ya fito ya zabe ta kuma aka tabbatar da ita, to bukatar sa ta biya, zancen korafi ba nasa bane, kamar dai Misalin wanda yake san mace mai kyau.

Yasir Ramadan Gwale 
30-06-2016

No comments:

Post a Comment