Saturday, May 19, 2012

Saudi-Bahrain: Karyar Iran ta kare!

Saudi-Bahrain: Karyar Iran ta kare!

A ranar sha hudu ga watan mayun wannan shekara ne (14th May, 2012) kungiyar kasashen Gulf Cooperation Council (GCC) wadan da suka hada da kasar Saudiyya da Bahrain da Hadaddiyar Daular Larabawa da Kuwait da Oman da kuma kasar Qatar, suka bada shelar da ta ke nuna hadewar kasar Saudiyya da Bahrain, a matsayin kasa guda mai bin tafarkin mulkin Sarauta karkashin Larabawa sunni. Hakika wannan hadewa muhimmin al'amari ne ga samun zaman lafiyar kasashen yankin Gulf. Hadewar dai tazo ne a yayin da aka samu akalla shekara guda 'yan shi'ah masu samun goyon baya daga Iran da Hizbolla ke ta kokarin yin juyin juya halin da zai kai ga kifar da gwamnatin Sheikh Hamad Bin Issa Alkhalifa a kasar ta Bahrain. Da farko dai sun fara ne da neman kawo sauyi a bisa yadda ake tafiyar da mulkin kasar, inda masarautar kasar ta bayyana gudanar da wasu sauye sauye da zasu baiyawa majalisar kasar dama mai yawa a cikin kundin tsarin mulkin kasar.

Ita dai kasar Bahrain, kusan za a iya cewa wani tsibiri ne da ya ware kadan daga cikin kasashen larabawa, kasar tana gab da kasar Saudiyya. ita dai wannan kasa ta Bahraina ta samu ne a shekarar 1783, lokacin da musulmi Ahlussunnah karkashin Gidan sarautar Alkhalifa suka fatattaki 'yan shi'ar Farisa. inda suka kafa daula mai bin tafarkin Sunni. Tun wancan lokacin ne kasar Farisa wadda ake kira Iran a yanzu take ta hakilon ganin cewar kasar Bahrain ta komo karkashin Daular Shi'ah, kasan cewar Bahrain ita ce kadai daga cikin kasashen larabawa da ta ke da mabiya addinin Shi'ah masu yawa. Kamar yadda muka sani kasar Iran kusan itace kasar da tafi kowacce kasa kusanci da kasashen larabawa bayan kuma ita ba kasar Larabawa bace, don haka kullin tunaninsu shi ne ya zasuyi su kwato kasar bahrain daga hannun gidan Sarautar Alkhalifa. Da kuma kokarin kawo tarzoma a daukacin kasashen larabawa, wanda suke gani wata dama ce a garesu ta su shiga su yada addinin Shi'a ga larabawa musulmi.

Tun bayan bore tare da zanga-zangar kasashen larabawa da ta samo asali daga Tunisiya, inda talakawa sukaci nasarar hambarar da gwamnatin zalunci ta Zainul Abedeen Ben Ali, abin ya rika yaduwa tare da goyon bayan munafukar kasar Iran da kuma 'yan Shi'ar Lebanon. haka abin ya ci gaba da yaduwa har ya isa kasar Masar wadda ita ce mafi kusanci da kasashen Turai da Amerika, inda suma talakawa sukaci nasarar hambarar da Shugaba Hony Mubarack duk kuwa da barazanar da ya ringayi musu, haka dai wannan guguwa ta yi ta kadawa a tsakanin kasashen larabawa, kuma itace tayi sanadiyar tafiyar Shugaba Ali Abdallah Saleh na Yemen da kuma kisan da akayiwa Shugaba Mu'ammar Ghaddafi na libya.

Haka dai wannan zanga-zanga ta cigaba da ruruwa har ta isa kasar Siriya, inda anan ne tafi yin muni ainun sama da kowacce kasa da akayi wannan zanga-zanga. Hakika gwamnatin Shugaba Bashar Assad ta yi amfani da wannan dama inda tayi ta kisan musulmi mabiya sunnah wadan da su ne suke da rinjaye a wannan kasa ta Siriya, anruwaito sosjoin gwamnatin Assad suna kai muna nan hare-hare akan garuruwan musulmi mabiya sunnah wadan da suka hada da Homs da Dar'a da Hama da Idlib da Aleppo da sauransu bayan kuma an yanke musu wutar lantarki da ruwan famfo, harkokin kasuwanci sun durkushe gabikidaya a wadan nan yankuna, duk kuwa wannan na faruwa ne da goyon bayan da Assad yake samu a fakaice daga kasar Iran da kuma kungiyar Hezbollah dake kasar Lebanon, kasancewarsa Dan Shi'a Alawiyyi, a gefe guda kuma shi Assad din yana kara samun goyon baya daga kasashen Turai da Amerika da Chana da kuma Rasha, duk wannan saboda suna tsoron kada su bari Assad ya sullube a sami wani shugaba daga cikin musulmi Sunni wanda zai kasance mai kishin addinin musulunci, wanda hakan zai kai ga tayar da maganar tuddan Golan da kasar Israela ta mamaye wanda shi shi Bashar Assad da Mahaifinsa Hafeez Assad suka kauda kai wa Israela. Sai kayi mamakin duk irin kurarin da kasashen turai sukeyi akan hakkin dan Adam, Bashar Assad yana kashe mutanansa amma suna rarrashinsa.

Duk da cewa kasashen larabawa sun goyi bayan wakilin majalisar dinkin duniya Mista Kofi Anan akan ya je kasar Siriya ya tattauna yadda za'a sasanta rikicin siyasar kasar. Amma wannan babu abinda akeyi illah yawan shakatawa da taron shan shayi, domin duk irin manufofin da Kofi Anan ya je da su Assad ya sa kafa ya yi fatali da su amma kuma ana tausarsa da cewa ya yi hakuri, a zauna akan tebur a sulhunta. shakka babu abin nan ne da ake kira Interest ya yi yawa akan kasar Siriya shi ya sanya kasashen Turai da Amerika suke ta jan-kafa akan Assad duk wannan yana kara bayyana karara irin yadda sakatariyar harkokin wajen Amerika Hilary Hoadharm Clinton da kuma jakadiyar Amerika a majalisar dinkin duniya Suzan Rice suke ta yin amai suna lashewa akan wannan batu na kasar siriya, da kuma 'yancin dan Adam.

Idan har da gaske suke akan yadda suke lallabar Assad, me yasa basuyiwa marigayi Saddam Hussein Allah yajikansa irin wannan ba? ko kuwa kawai domin shi musulmi ne sunni, shakka babu wannan a bayyane take cewa Amerika da NATO sun afkawa Saddam Hussein saboda kasancewarsa Musulmi sunni, domin dukkan irin bayanan da mista Hatz Blick ya bayar sun nuna cewar Saddam ba shida wasu makamai masu hadari ko guba. A gefe guda kuma ana ta kokarin nunawa duniya cewa akwai baraka tsakanin Amerika da Iran, sanin kowane cewar da hadin bakin kasar Iran dari bisa dari aka yaki Saddam, kuma 'yan shi'a su Muktada Al-sadar da suke samun goyon baya daga Iran suka ci karensu babu babbaka duk da ana nuna cewa akwai tsamin alaka tsakaninsu da Amerika, koma dai meye Hausawa sunce shi munafurci dodo ne mai shi yake ci, don haka komai tsawon lokaci zai bayyana.

Idan kuma muka dawo batun kasar Bahrain, dole ne mu yabawa sarkin Qatar Sheikh Hamad Bin Jassim Althani da kuma shi kansa sarkin Bahrain Shiekh Hamad Bin Issa Alkhalifa da kuma Sarki Abdallah Bin Abdulazeez Ali-Saud na Saudiyya, hakika wannan namijin kokari ne sukayi na kokarin dinke barakar wannan yanki. kuma muna fatar watan wata rana a samu yanayin da zai kai ga kafa kasar larabawa kwaya daya (United State of Arabia), wadda muna sa ran ita zata kai ga kafa shugabancin musulmi guda daya a duniya, kuma muna nan muna fatan ganin kasar Iran ta komo karkashin Musulmi sunni, a kusa ko a nesa. domin sanin kowa ne cewa babu wata kasa a yanzu da take mafi hadari a duniya sama da kasar Iran, domin duk wani munafurci da fadi tashi da su akeyi, ya Allah ka wargaza aniyarsu ka rusa lamarinsu, ka hansu sakat.

kaicon tsufa, hakika Tsufa wata cuta ce da batada magani, kuma babu yadda dan Adam zai yi da rayuwa sai tsufa ya riskeshi, tsufa ya zowa Sarki Abdallah Bin AbdulAzeez Al-Sa'oud na Saudiyya a lokacin da duniyar Larabawa da ta musulmi suke da bukatar shawarwari da tunaninsa, da hange irin nasa, muna addu'a ga Khadumul Haramainissharifain, Allah ya kara masa lafiya da kwanciyar hankali, Allah ya sanya albarka acikin rauwarsa, hakika ya yi hidima ga dakin Allah mai alfarma da masallacin manzon Allah dake madina, Allah ya cika a mizaninsa, Allah ya jakwanansa. Muna kuma Addu'ar Allah ya yafe masa laifukansa wanda ya aikata bisa kuskure da wanda ya aikata bisa sani ko ajizanci. Allah ya taimaki Masarautar Sadiyya da Addinin Musulunci baki daya. ya Allah ka nuna mana ranar da za'a kawo karshen shi'ah a wannan duniyar.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com  

No comments:

Post a Comment