Tuesday, July 22, 2014

Shin Akwai Wadan Da Za Su Iya Tunkarar Israela?

Obama Da Netanyahu
SHIN AKWAI WADAN DA ZA SU IYA TUNKARAR ISRAELA?

IIsraela tafi karfin kowa a kasashen Musulmi ta fuskar karfin Makamai da karfin fasaha. Hatta kasashe irin su Pakistan da suka mallaki Nukiliya babu yadda zasu iya da Israela ballantana kuma kasashen larabawa da galibi Israelawa ke kera musu makaman da suke saya a Amurka. Dan haka dole kowa ya yi Shakkar Israela. Abu mafi muhimmanci shi ne mutane da shugabannin kasashen Musulmi su komawa Alkur'ani su karanta Me Allah ya fada akan Yahudawa. Sannan a koma zuwa ga Allah, a yi riko da dukkan sabubba na karbar addu'ah da kuma cin Nasara a rayuwa.

Amma zance na gaskiya Israela tafi karfin kowa. Duk wasu da ake zaton za su iya yin wani abu akan Isarela suma sun san babu abinda zasu iya illai kawai surutai a gidajen Radiyo da Talabijin. Majalisar dinkin duniya a aljihun Amerika ta ke babu wani abu da take aiwatarwa face ra'ayin Amerika. Haka kuma, ita Amerikan kanta a cikin tafin hannun Israela ta ke, dan haka duk wani surutu da za'ai a majalisar dinkin duniya akan Israela duk zancen banza ne.

Sanin kowa ne babu wani hakki na bil Adama da Israela bata taka shi ta murje a Ghazza ba, amma wa ya isa yace Uwar Sarki Mayya ce? Shi ya sa sai ayi ta kewaye kewayen cewa ai Israela na da damar kare kanta daga hare-haren rokokin 'yan Hamas, mutanan da galibin makaman da suke harbawa a sararin iska suke watsewa.

Wasu da dama kuma kan zargi shugabannin kasashen Larabawa da cewa sun kasa yin wani abu a Ghazza. NA farko dai ya kamata mu sani duk wani abu da larabawa zasu yi akan Ghazza ko Israela to bai wuce SURUTU na fatar baki ba, domin sunfi kowa sanin wace Israela da irin karfin da ta ke da shi ta fuskar karfin Makamai. Israela kadai tafi dukkan kasashen gabas ta tsakiya karfin Makamai. Sai dai kawai idan za ai siyasar yarjejeniya kaji Hizbola na cika baki alhali babu abinda zasu iya, su kuma Iran da yake munafukai ne sai su ce ai sune suke taimakawa Palasdinawa da makamai, indai gaskiya ne muji karajin makaman da Tehran ke da su a biranen Ashdod da Tel Aviv.

Abinda na yi Imani kadai zai iya rusa Israela shi ne karfin ikon Allah, da kuma karfin Imani na wadan da ake zalunta. Israela idan tafi karfin kowa bata fi karfin Allah ba, fatan kawai shi ne mu dage da addu'ah mu kuma yi riko da sabubban karbar addu'ah, sannan a gefe daya surutan da ake yi a cigaba duk da babu wani tasiri da yake yi, dan in duk duniya zata cika da zangar-zangar kyamar Israela to su ko a jikinsu wai an tsikari kausasa.

Muna rokon Allah ya kaiwa Palasdinawa masu rauni dauki, Allah ya amintar da su. Su kuma Yahudawa Allah ya fimu sanin abinda yafi cancanta da su, Allah ya yi musu ninkin ba-ninkn abinda suka yiwa Musulmi na cin zali.

YASIR RAMADAN GWALE
22-07-2014

1 comment:

  1. HELLO EVERYONE.. FEW MUNINETS TO REDY THIS INFOR ON HERPES CURE 2018..
    2017 MY MOTHER WAS DIAGNOSED OF HERPES/ KNOWN AS GENITAL WARTS ,I SPENT A LOT OF MONEY ON HER MEDICATION TILL A POINT I EVEN LOST HOPE,BECAUSE MY MOTHER WAS GRADUALLY DYING AND LOST HER MEMORY TOO, I WAS SO DESPERATE TO GET MY MOTHER BACK TO NORMAL, ONE DAY MY UNCLE WHO LIVES IN LONDON UNITED KINGDOM TOLD ME ABOUT DR OLIHA ,WHO HELPED HIM GET RID OF HERPES /GENITAL WART WITH HERBAL MEDICINE AND HIS HERBAL SOAP ,I WAS SO SHOCKED WHEN HE TOLD ME ABOUT THIS ,ALTHOUGH I NEVER BELIEVE IN HERB BUT, I KEEP TO BELIEVE BECAUSE MY UNCLE CAN'T TELL ME LIES WHEN IT COMES TO HEALTH CONDITION I CONTACTED DR OLIHA VIA HIS EMAIL; OLIHA.MIRACLEMEDICINE@GMAIL.COM , YOU CAN TALK TO HIM VIA CALL OR WHATSAPP MESSENGER ON +2349038382931 , HE REPLIED AND ASK ME TO SEND MY HOME ADDRESS AND MY MOTHER'S DETAIL AND THEN I PURCHASED THE HERBAL MEDICINE,SENT ME THE HERBAL MEDICINE THROUGH COURIER SERVICE, WHEN I RECEIVED THIS HERBAL MEDICINE USED IT FOR 2 WEEKS, AND 4 DAYS OF USAGE THE WARTS FELL OFF, MY MOTHER I NOW TOTALLY CURED AND MY MOTHER IS LIVING FREE AND HAPPY AGAIN. YOU CAN TALK TO DR VIA HIS MOBILE NUMBER OR WHATS APP HIM ON +2349038382931  ALL THANKS TO DOCTOR DR OLIHA  

    ReplyDelete