Sunday, June 21, 2015

Tsokaci Kan Azumi #Ramadan 2015


TSOKACI KAN AZUMI #RAMADAN 2015

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, Yace duk wanda ya ciyar da mai Azumi yana da kwatankwacin ladansa. Da yawan al'umma da sun fahimci wannan magana ta Manzon Allah SallLlahu Alaihi Wasallam, da kowa ya kasance mai kokarin ciyarwa, ba wanda ake ciyarwa ba. Haka kuma, Manzon Allah tsira da Amincin Allah su kara tabbata a gareshi yana cewa, ku fanshi kanku daga wuta ko da kuwa da tsagin dabino ne.

Babu shakka wadannan maganganu guda biyu suna nuna mana tsananin kwadaitarwa da ciyarwa da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, yayi mana umarni da su. Sai dai kadan ne daga cikin al'ummarmu suka fahimci wadannan maganganu biyu masu matukar muhimman. Allah ka bamu ikn ciyarwa da dan abinda muka mallaka.

Yasir Ramadan Gwale
21-06-2015

Wakar Gaskiya Ta Marigayi Sa'adu Zungur



WAKAR GASKIYA TA SA'ADU ZUNGUR

In za Ka faďi, faďi gaskiya,
Kome taka ja maka ka biya! "
Sai mu gode Allah shi ďaya,
Don Shi ne sarkin gaskiya.

Ya mallaki dukkan talikai,
Na kwari da tudu da samaniya.

Da mutun, aljan damala'ika,
Dabbar sarari Da ta Malaya.

Mulki, iko, daula duka,
Na ga Sarki Allah shi ďaya.

Shi ya ke ba wanda ya so duka,
Ya sarautu a lardin duniya.

Shi ya ke karbe ta ga talikai,
Don ya ďanďani wahalan duniya.

Shi ka girmama Wanda ya so duka,
shi ka sanya waďansu su sha wuya.
Shi ka cusa dare a cikin wuni,
Kuma ya zaro hasken dariya.

Shi ka rayawar mamaci,
Shi ke kashe mai rai, shi ďaya.

Ikonsa a kan kome ya ke,
A ruwa Da tudu da samaniya.

Alwakilu, mu dogara duk garai,
Zahirinmmu Da boye a zuciya.

Mu amince, zai mana taimako,
Na hakika inda majaziya.
-(Mohammadu, 1972) KA KOYI KARATU 4)

Yasir Ramadan Gwale
21-06-2015

Tuesday, June 16, 2015

Albashi Da Alawus Din 'Yan Majalisu


ALBASHI DA ALAWUS DIN 'YAN MAJALISU 

Indai da gaske wannan canji an same shi domin al'ummar kasa, da  sake gina kasa da hidimtawa al'umma, to ya kamata a zaftare wannan mahaukacin Albashi da alawus na 'yan majalisu. Kai jama’a! Ana maganar wasu jihohi ba su da kudin da zasu yi Albashi,  amma ace kudade masu tarin yawa suna shiga aljihun 'yan majalisu ba tare da sun yi wani aiki mai yawa ba da suka cancanci wannan kudi. Wannan abin yayi kama da yiwa 'yan Najeriya fashi, ace wadannan mahaukatan kudade zasu dinga shiga aljifan 'yan majalisu duk Shekara. Gaskiya da sake.

YASIR RAMADAN GWALE​
16-06-2015

Sunday, June 14, 2015

Su Waye Ke K'ok'arin Ganin Bayan Dr. Ahmad BUK?


SU WAYE KE K'OK'ARIN GANIN BAYAN DR. AHMAD BUK?

Kamar yadda labari ya bazu cewar Khalifan Tijaniya Isyaku Rabi'u da sauran jagorancin  dari'kar sun shigar da Babban Malamin Hadisi na Tudun Yola Dr. Ahmad Ibrahim BUK k'ara wajen Shugaban shiyya ta d'aya ta rundunar 'yan Sanda ta k'asa dake Kano, Tambari Yabo Mohammed akan zargin sa da suke ya aibata Shehunsu Inyass Kaulaha! 

Babu shakka wannan abu da ya faru, mun ji dad'i kuma mun yiwa Allah godiya domin ya tabbatar da cewar Dr. Ahmad ba k'arya yayi ba da yayi rantsuwa da Allah  yace "wallahi yadda suke girmama Shehunsu basa ganin Girman Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam haka" hakika a wannan marra, Allah ya kubutar da Malamin Hadisi Dr. Ahmad ga masu ganin baiken kalaman sa. 

Haka kuma, a cikin raddin da Dr. Ahmad d'in yayi bayan waccan tab'argaza da kafurci da Abul Inyass yayi da sunan Tijaniya, Malamin Hadisin Dr. Ahmad ya kalubalanci 'yan Tijaniya akan su zo a zauna a gidan Radio a yiwa al'umma bayani, yace Darul Hadith zata biya kudin a ji shin sharri ne ko karya ake yiwa Inyass Kaulaha, amma suka k'i amsa wannan gayyata suka b'ige da bita da k'ulli.

Ni ina ganin abinda ya kamata su Khalifa Isyaku Rabi'u suyi kenan, na amsa waccan gayyata da shi Malam yayi ya kuma ce zasu biya kudin ko awa nawa za a yi a Freedom Radio da Rahama da Radio Kano, domin bayyanawa al'ummar da suke ganin abin ba haka yake ba. Ko kuma su 'yan Tijaniya su kare abin da hujja su ce ba haka bane.

A dan haka, wannan abu, babu abinda zai k'ara illa k'ara tsiraita Tijaniya da kuma d'aukaka darajar Malamin Hadisi Dr. Ahmad Ibrahim BUK. Idan kuma sun gayawa Tambari Yabo cewar Malamin Hadisin ba d'an Najeriya bane, sai muce ai Shima Inyass Kaulaha  din ba dan Najeriya bane, mutumin kasar Senegal ne.

A sabida haka, muna kara jaddada cewar wallahi summa tallahi Martaba da Darajar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam tafi ta uban kowa, kuma tafi ta ko wanne irin Shehu na da da na yanzu. Kuma Alhamdulillah wannan lokaci ne da al'umma zata fahimci hak'ik'anin abubuwan da suke cikin Tijaniya da littattafan Inyass Kaulaha. 

Malaminmu Dr. Ahmad Ibrahim muna tare da shi kuma muna goyon bayan dukkan maganganun da yayi na rushe wannan kafurci da yake cikin Tijaniya. Wanda duk ya kuduri aniyar ganin bayan Malamin Sunnah ko waye Ya Allah ka nuna mana karshensa, Ya Allah ka bakanta musu ciki da samun d'aukakar Sunnah, Allah ka dirkake Bid'ah da dukkan dangoginta. 

Daga karshe kuma, muna kira ga Babban Kwamandan Hisbah na Kano Mal.Aminu Ibrahim Daurawa, kamar yadda ya bada sanarwa cewar hukumarsa ta karbi gabarar wannan Shari'ah da aka kai wannan zindiki Batijane da ya zagi Manzon Allah Sallallahu was Alaihi  Wa Sallwm cewar muna nan muna bin bahasinsu. 

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam na dukkan Musulmi ne dan haka ne al'umma a ciki da wajen jihar Kano hankalin su ya tashi akan wannan batu. A bisa jagoranci da Hukumar Hisbar Kano suka ce sunyi na wannan Shari'ah zamu dinga matsa muku lamba har sai an hukunta wannan zindikin, idan ba haka ba kuma kun yaudari jama'a kuma Allah ba zai kyale ku ba.

Ya Allah ka tozarta duk wanda ya tozarta ManzonKa Sallallahu Alaihi Wa Sallam akan Shehunsa. Ya Allah ka la'anci duk wadan da suka fifita wani Shehunsu akan ManzonKa Sallallahu Alaihi Wa Sallam. Allah kayi dadin tsira a gareshi da Alayensa da Sahabbansa da wadan da suka biyo Tafarkin su da kyautatawa har  ya zuwa ranar sakamako. 

Yasir Ramadan Gwale
14-06-2015

Friday, June 12, 2015

Mutuwa Rigar Kowa


MUTUWA RIGAR KOWA

A 'yan kwanakin nan naga mutane da yawa suna ta bayar da labarin rasuwa nan da can, wasu iyayansu wasu 'yan uwansu, wasu 'ya 'yansu wasu dangi wasu Abokai da sauransu da dama Allah ya jikan Musulmi.

Hakika nima a Makon jiya da wannan satin anyi rasuwa uku da ta girgizani ainun. Abokinmu Muzammil Ahamad Jihar yaro matashi da kuma wasu Abokanmu su biyu da suka rasu sakamakon kad'e su da mota tayi a Makon da ya wuce, rasuwar da ta girgiza mutane da yawa a Khartoum.

Haka kuma a wannan satin na samu labarin rasuwar Shamsiyya Lawal Gwale, Alal hakika naji wannan rasuwa sosai, tare aka sanyamu a Gwale Primary da Shamsiyya, muna mutunci da zumunci har zuwa lokacin da tayi aure. Ina yiwa mijinta Basiru Miller Gwale ta'aziyar rasuwar ta, da kuma 'yan uwa da dangi musamman Babban yayanmu Pharm. Ibrahim Lawal​ Allah ya jikanta ya gafarta mata.

Yadda muke karanta labarin rasuwar wasu haka muma watarana za'a karanta labarin rasuwar mu. Zato zo mana ko mun shirya ko bamu shirya ba, Malamai suka ce babu wani wa'azi ko nasiha ko Jan hankali da ya kai mutuwa, domin ita ce, mai yanke komai, wanda duk ya Rasu to shi kenan haihata haihata tasa ta riga ta kare.

Dan haka irin wadannan labari da muke samu na rasuwa nan da can, tabbas, wata rana muma zata zo kanmu, muna sane ko mun gafala. Dan haka muji tsoron Allah mu sauya halayenmu daga munana zuwa kyawawa, daga masu zafin zuciya zuwa masu saukin rai,  daga masu tsanani zuwa masu hakuri. 

Ya Allah ka jikan mamatanmu,  ka yafe musu laifukan su da dukkan kurakuransu, Allah ka sadar da su da RahamarKa, mu kuma da muka Rage Ya Allah ka sa mu cika da Imani, Allah kasanmu kasan halayenmu, Allah ka yafe mana laifuka da kurakuran da mukai maka muna sane ko mun gafala, Allah kai mai afuwa ne kana son Afuwa, Allah kai mana afuwar laifukanmu,  Allah ka lullubemu da RahamarKa. 

Yasir Ramadan Gwale​
12-06-2015

Tuesday, June 9, 2015

Shugabancin Majalisa: Lissafi Ya Kwacewa Shugabancin APC


ZAB'EN SHUGABANCIN MAJALISA: LISSAFI YA K'WACEWA SHUGABANCIN APC

Abin mamaki ne a wannan lokacin uwar Jam'iyyar APC ta kasa ta nuna fushi ko damuwa akan zaben da akaiwa Sen. Abubakar Bukola Saraki​ da Dogara Yakubu a matsayin sabbin shugabannin majalisar Dattawa da ta wakilai. Sune fa Shugabannin APC suka dinga bin su Bukola da Gwamnonin PDP biyar da sukai mata tawaye gida gida suna rokonsu Allah su shigo APC, suka amsa wannan kira suka shiga aka nuna musu babu wani bambanci kowa daya ne.

Wadan da suka sha wahalar kafa APC akai fatali da su, aka nuna su ba komai bane, aka fusatasu da gangan suka d'an su fice, aka nuna su Bukola sune mutanan kirki. Sai yanzu da aka kafa Gwamnati ake neman kwashe musu kafa, su Bukola suka had'a kansu suka samarwa da kansu makoma, sannan ne shugabancin APC na kasa suka fahimci cewar wadannan shigogo ne a cikin jam'iyyar? 

Ba shakka wannan zabe da akaiwa Bukola Saraki da Yakubu Dogara ya dace, domin ko babu komai ya nuna tsantsar Demokaradiyya, domin hakan ya tabbatarwa duk wani wanda yake jin cewar shi ne ya mallaki APC sai abinda yake so shi za ai, to zai gane cewa kan mage ya waye, ba kowa bane Bayerbe. Idan ana batun Demokaradiyya to tilas a bar kowa da ra'ayinsa. 

Wannan Zabe da akaiwa Bukola Saraki da Dogara Yakubu yana bisa doron Demokaradiyya, hakan kuma ya dace. Ai idan ba lissafi ne ya kwacewa shugabancin APC ba, jagororinta a baya sune suka zuga 'yan majalisun ACN da ANPP da CPC da wasu daga cikin mambobin PDP akan su bijirewa 'yan takarar da PDP ta tsayar su zabi  Aminu Waziri Tambuwal, kuma akai hakan. Shin tsammaninsu PDP bata dauki darasi akan abinda ya faru ba?

A ganina wannan shi ne tsantsar Demokaradiyya,  domin samun wannan shugabanci zai taimakawa shi kansa Shugaban kasa Muhammadu Buhari​ wajen aiwatar da aikin sa ba tare da tunanin cewar wani mutum shi kadai ra'ayi sa ya rinjaye na kowa ba, kuma abinda yake so shi za ayi. 

A dan haka wannan babu abinda yake nufi zai tabbatarwa da 'yan Najeriya cewa mutum daya ba zai iya saka al'ummar Najeriya a aljihunsa shi kadai ba, ya zama ba abinda zai faru a Najeriya sai abinda yake so. Ina amfani da wannan damar wajen taya sabon Shugaban majalisar Dattawa Bukola Saraki da mataimakinsa Ike Ikweremadu murnar wannan zabe da akai musu, haka shima Dogara muna taya shi murna.

Yasir Ramadan Gwale​ 
06-06-2015 

Ashe Dogara Ma Ya Kada Femi Babanjamila


ASHE DOGARA MA YA KADA FEMI BABANJAMILA??
Yanzu dai babu ko tantama cewar, Shugabannin Jam'iyyar APC ba su da wani iko akan 'yan majalisun da suka ci zabe karkashinsu, dazu a majalisar Dattawa an Kada wanda jam'iyar ta nuna inda aka zabi Abubakar Bukola Saraki tsohon dan PDP wanda ya shigo APC daga baya, bayan ta gama nuna.
Ya zu ma gashi a majalisar wakilai an zabi sabon Kakakin Majalisar Hon. Dogara Yakubu, wanda shima tsohon dan PDP daga jihar Bauchi, ya shiga APC ne bayan D ta gama nuna. Wannan yake nuna cewar 'yan majalisun guda biyu sun kawo karshen fad'a a jin da Jagoran APC na kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu yake da shi a jam'iyar. Zamu jira muga irin yadda itama majalisar karkashin Dogara zata yi nata rabon mukamai din.
Ko za'a samu jituwa tsakanin Bangaren Majalisar wakilai karkashin Jagorancin Saraki da Dogara da kuma Majalisar Zartarwa karkashin sabon Shugaban kasa. A baya dai mu ga yadda akai zaman do ya da man ja tsakanin Goodluck Jonathan Da majalisar wakilai.
Yasir Ramadan Gwale 
09-06-2015

KWAD'O: Sabon Shugabancin Majalisar Dattawa


KWA'DO: SABON SHUGABANCIN MAJALISAR DATTAWA

Wannan sabon shugabanci na majalisar Dattawa da aka samu a yanzu bai zowa da dama da mamaki ba, domin tuni masu sharhi akan Shugabancin Majalisar sukai hasashe abin da ya faru. Kamar yadda Jam'iyyar APC mai mulki ta bayar da sanarwar fitar da wadan da take son a zab'a a sabon Shugabancin Majalisar, inda suka zabi Sen. Ahmed Lawan A Matsayin Shugaban Majalisa da kuma George Akume a matsayin mataimakina,  haka kuma APC sun zabi Hon. Femi Babanjamila a matsayin dan takarar shugabancin majalisar wakilai.

Kwastam yau da aka tashi zabe, a cikin sanatoci 108 da ake da su, an samu guda 57 sun zabi Abubakar Bukola Saraki​ a matsayin sabon Shugaban Majalisa Dattawa, zab'in da tun farko ya sabawa Shugabancin APC. Hakan dai na nufin sanatoci 51 da basu zabe ba, ba zasu iya wani katabus a a canza wannan sabon shugabancin ba, abin mamaki shi ne yadda PDP ta samu manyan mukaman Majalisar guda biyu, wato mataimakin Shugaban majalisar Dattawa da kuma Shugaban masu rinjaye da ake kira Senate Leader.

Da akwai alamar turka-turka a wannan shugabancin na majalisa, domin David Mark tsohon Shugaban Majalisa ya samu mukamin Senate Leader duk kuwa da cewar ya fito daga PDP da take a matsayin jam'iyyar Adawa a majalisar, abinda kowa zai zura ido ya gani shi ne yadda za'a nada Shugaban marasa rinjaye na majalisar,  shin zai fito daga PDP ne ko kuma daga APC?

Idan har PDP ta sake samun mukamin Shugaban marasa rinjaye bayan samun shugabancin masu rinjaye to lallai PDP nada karfi a wannan majalisa ta takwas, a gefe guda kuma, idan APC ta karbi Shugaban marasa rinjaye to ba shakka ankai keyarta kasa, domin a matsayinta na jam'iya ma mulki ta koma mai adawa a majalisar duk kuwa da cewar ita ke da rinjaye. Tuni dai sabbin shugabannin majalisar da suka had'a da sabon Shugaba Saraki, da mataimakinsa Ike Ikweremadu da Shugaban masu rinjaye David Mark suka sha rantsuwar kama aiki.

Kada mu manta kowa ce jiha a Najeriya nada wakilcin sanatoci uku yayin da Abuja ke da sanata guda daya, haka kuma, kwanakin baya an bada sanarwar rasuwar sabon Sanatan APC daga jihar Borno, abinda yake nuna sanatoci da suke kasa sune 108. Zamu ga yadda wannan sabon Shugabancin Majalisa zai wanye da bangaren zartarwa.

Yasir Ramadan Gwale 
09-06-2015

Friday, June 5, 2015

Tatsuniyar 'Yan Shiah Kan Salman Rushdie


TATSUNIYAR 'YAN SHIAH AKAN SALMAN RUSHDIE 

'Yan Shiah sun kasance suna yaudara mutane da yawa ta hanyar gaya musu cewar, akwai wani mutum da yayi kalaman batanci ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam da addinin Musulunci mai suna Salman Rushdie, wanda yake zaune a England. A dan haka Shugaban addininsu na Iran Ayatoulla Kumeini ya sanya lada na rabin dukiyarsa ga duk wanda ya kamo ko ya sare masa wuyan Salman Rushdie. 

Ayi ta nunawa kauyawa da basu fahimci Shiah ba, wai irin kaunar da su 'yan Shiah suke da ita ga Ahlulbaity da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam. Kaga mutanen da aka yaudara suna ta kabbara suna ihu tare da jinjinawa Khumeini. Amma kuma wannan a bayyana take a garemu cewar yaudara ce tsagwaronta suke yi. Haka su Zakzaky ke ta yiwa mabiyansu wannan Tatsuniyar akan Salman Rushdie. 

Sai gashi 'yan Tijaniya a Kano sun zagi Manzon Allah Sallallahu Alaihi WaSallam,  amma bamu ji Zakzaky ya bayar da rabin dukiyarsa ga wanda ya kamo ko ya sare wuyan Abdul Inyass ba. Wannan na daya daga cikin dalilin da ke tabbatar wa da al'umma karya da yaudara da 'yan Shiah da 'yan darika ke yi na cewa sune masu kaunar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam. 

Wallahi duk wanda ya kama bin hanyar wani ba Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam ba, zai yi nadamar da bazata amfani shi ba a ranar gobe kiyama. Bin Tafarkin Manzon Allah shi kadai ne dacewa, Riko da Sunnah shi ne hakikanin shiriya. Allah ka tabbatar da mu akan bin Sunnar ManzonKa Sallallahu Alaihi Wa Sallam. Allah kayi dadin tsira a gareshi da Alayensa da Sahabbansa da wadan da suka biyo Tafarkin su da kyautatawahar ya zuwa ranar sakamako.

Yasir Ramadan Gwale 
06-06-2015

Thursday, June 4, 2015

MARTANI: Goodluck Jonathan Da Boko Haram


MARTANI: BOKO HARAM DA GOODLUCK JONATHAN 

Daga Ibrahim Abu Mufidat​

A rubutun da Malam Yasir Ramadan Gwale yayi jiya Laraba 3 ga watan Yuni, naga mutane da yawa sun kasa fahimtar abun kamar yadda Yasir ya haska mana, da yawa suna maganar an janye sojoji kafin harin da 'yan ta'add a suka kai a kauyen Buni-Yadi dake jihar Yobe, abinda ya kamata masu zargi su sani shin shi Jonathan ne yake kwamandin din su sojojin a wajen? Ba jagororin kusa dasu za a zarga ba? Duk da cewar Shugaban kasa shi ne, shugaban kwamandan askarawan Najeriya baki daya, amma kowa yasan a matsayinsa na shugaba yana magana ne da shugabannin sojoji ba daidaikun kwamandoji ba, haka kuma, muna gani har korar irin wadannan sojojin akeyi a yanzu bayan anyi bincike an gano cewar haka kawai suka dinga guduwa? 

Haka Kuma, bari na gayawa muku wani abu da baku sani ba, tun usli sojojin Buni-Yadi tsorata suka yi suka gudu, bayan da suka ga baza su iya tunkarar mayakan Boko Haram ba, saboda karfinsu, sannan anan zan bijiro da wata tambaya, bayan an kai harin Buni-yadi an kai sojoji garin da dama, wata rana Boko Haram suka zo sukai musu kawanya suka kashe su su da 'yan sanda kusan hamsin har kwamandan su bai tsiraba hadda DPO na 'yan sanda gaba daya duk aka kashe su, to shima kenan Jonathan ne yasa akashe sojojin kasarsa? 

A Pakistan kungiyar Taliban sun shiga makaranta sun kashe matasa kusan dari biyu (200) su mai yasa ba'a cewa Gwamnati ce take sa a kashe su sai mu a Najeriya? Idan fa kukayi tunani Jonathan yazo ya tarar da Boko Haram ne fa ba wai sai da yazo suka zo ba, mai yasa ba a zargin tsohon shugaban kasa marigayi Umaru Musa 'YarAduwa da aka fara abin lokacin sa? Yakamata mu sani babu abin da ya zamto sanadin rashin tazarcen Jonathan kamar Boko Haram, shima a bangarensa na kudancin kasarnan zargi suke cewa 'yan Arewa ne suka kirkiri Boko Haram don a dagula masa lissafin Gwamnatin sa, shi wanne irin mutum ne zayyi sanadin faduwar mulkinsa da kansa? Da sunan Boko Haram! 

Duk kishinka da son Buhari, an sha tambayarsa bai taba cewa yana zargin Jonathan da hannun ba, sai dai yace akwai sakaci na daukar matakin da ya dace daga Gwamnati, kuma duk masu irin wannan tunanin abu biyu ke damunsu, (1) Rashin adalci da kuma (2) Jahilci. Na farko, basu san su waye Boko Haram ba, saboda duk duniya tana fama da irin wadannan yan ta'adda, misali ga shi nan a kasar Mali, sai da suka kwace fiye da rabin kasar suka kafa abin da suke kira "daularsu", kuma lokacin har Boko Haram sunje sun tayasu yakin tsawon wata shida sukayi suna rike da fiye da rabin kasar, kuma abin sha'awa cikin sojojin da suka yi kokarin fatattakarsu karkashin jagorancin Faransa, har da sojojin Najeriya, to abin tambya shine, ya za'ayi su yan jihadin Mali su yarda Boko Haram su shiga cikinsu suna fada tare, bayan sun san cewa Jonathan ne yake daukar nauyinsu, kuma ahannun guda ga sojojin da Jonathan ya turo suna kashe su a Mali? 

Kuma wani rashin adalci mafi girma da akewa Jonathan shine, idan sojojin Najeriya suka samu nasara kan Boko Haram ko suka hanasu shiga gari, ba a jingina wa Jonatan nasarar, amma idan sun gudu ko an samu nasara akansu sai ace Jonathan ne yace su gudu, kai sai ka dauka kamar sojojin da suke kokari bana Najeriya bane, sai wadan da suke guduwa sune na Najeriya. 

Misali 'yan Boko Haram bayan sun kwace garin Goza suka kwashi makaman da basu taba mallaka ba,  hankali ya tashi sosai, suka tunkaro Maiduguri gadan gadan, suka fara zuwa bama ko awa biyu basu yi ba suka fatattaki sojojin Bama, saura gari daya ne ya rage musu tsakanin su da Maiduguri, shine Konduga, amma da yake sojojin konduga sun tsaya sun bayar da rayuwarsu, sai da suka yiwa Boko Haram kofar raggo sukai musu barna mai yawan gaske, saboda haushi da fusata da Boko haram suka yi suna ganin gari daya ne ya rage su shiga maiduguri, sukayita zuwa sojojin kondiga na kashesu, arana daya tak, sai da suka je sau biyar, an kashe su sunfi dubu aranar, har aka kama mataimakin shekau wanda hotonsa ya shahara ana cewa shekau din ne, anan kuma aka kashe mai daukar musu video, kuma aka kwace dukkan makaman da suka kwato daga Bama da Goza, amma baza ka taba jin ana jingina irin wannan nasarar ga Jonathan ba, sai ake cewa wai Goza cewa akai sojojin su fita, to shin Konduga fa, yace su fita sunki kenan? 

Abinda da yawa daga mutane suka kasa fahimta shi ne, idan akazo ana lissafin nasara wallahi sojojin Najeriya sunfi samun nasara kan Boko Haram, sama da yadda Boko Haram ke samu akansu, don har yanzu Boko Haram burinsu shine su dawo Maiduguri su kwaci Markazin su, abin da yasa suka haukace suke kashe kowa da kowa kenan, haushin rashin nasarar da suke samu shi ne, sai suke bi suna kashe mata da yara da kauyawa, kuma ko kai yanzu akace duk inda kaga mutum wanda ba kai ba ka kashe shi, to kafin a kama ka za a dade, saboda Allah yayiwa dan Adam yawa abayan kasa, da yawa daga wasu kauyuka ma Gwamnati bata san da su ba, mu Najeriya  duk inda kaga hanya cikin daji komai duhun dajin to idan kabita sai ka samu mutane suna rayuwa a wajen, to irin wadannan nefa Boko Haram suke gwada nasararsu akansu. 

Don haka ni anawa ra'ayin, yadda naga Jonathan ya shirya zabe mafi tsabta kuma ya miqa mulki cikin ruwansanyi, yakamata koda kana masa zargi abaya na rashin son zaman lafiya, to kagane ayanzu haka da yayi shi mai son zaman lafiyane da dorewar Najeriya kasa daya al'umma daya.

Yasir Ramadan Gwale 
04-06-2015

Wednesday, June 3, 2015

Boko Haram Da Goodluck Jonathan


BOKO HARAM DA GOODLUCK JONATHAN
Da sannu gaskiya zata bayyana. Ada idan muka ce Jonathan ba shi ne Boko Haram ba wasu gani suke wannan magana tamkar Ridda ce, ai bayadda za'a ce Jonathan ba shi ne ke kashe mu ba, a tunaninsu ai tsabagen kiyayya ce ta sanya Jonathan ke kashe mutanan Arewa.
Mutane da yawa sun shiga rudu akan hakikanin al'amarin Boko haram, aka kasa yiwa Jonathan adalci akan Boko haram. Mutane, ciki har da masu ilimi da suke tara jama'a su yi musu huduba, zaka ji suna rantsuwa da Allah cewar Jonathan ne ke kashe mutane da sunan Boko Haram, kawai sabida sunga wannan ce hañya mafi sauki ta neman suna da tara jama'a.
Mutane da dama sun dinga yad'a wata magana wadda ta samo asali daga Gumsu Sani Abacha, tana cewar, tsohon Shugaban kasa Marigayi Abacha yana cewar "duk wani rikici da gwamnati ta kasa shawo kansa cikin awa ashirin da hudu to akwai hannunta a ciki" wannan magana ta yadu kamar wutar daji, kuma ta zauna a zukatan mutane da yawa.
Daga acikin abin da zai fi bada mamaki shi ne yadda har mutanan da suke a yankin da wannan fitina ke faruwa zaka ji suna zargin Jonathan da cewa da hannunsa wadannan abubuwa ke wakana. Wasu har anan facebook suka dinga karairayi da kaucewa gaskiya, da d'ora laifi ga Jonathan amma kuma yanzu sun fara lashe aman da suka yi akan zargin da sukaiwa Jonathan na zalinci.
Kamar yadda muka sha fadi a baya, wannan batu samo bakin warware shi yana da alaka da sai mutane sun gamsu akwai Boko haram kuma kuma 'ya 'yan Musulmi ne da suke ikirarin addini sannan su gamsu cewa ba Jonathan bane, sannan hakikanin gaskiya zata bayyans a shawo kan abun. tare da abokan gwagwarmaya irinsu Yamai Muhammad Buhari da Sule Abbati mun sha nanata wannan kira sau da yawa a baya, abinda mutane suka ki yadda su fahimta da gangan.
Dukkanmu munyi tarayya wajen cewar matakan da ake dauka a tunani irin namu ba su ya dace a dauka dan magance rikicin ba, sannan shugaban kasa na lokacin Mista Jonathan duk munyi tarayya akan cewar yana da sakaci wajen daukar matakan da suka dace. Amma wasu da dama suna ganin babu yadda za'a ce Jonathan bai da hannu a wannan rikici, Musulmi shi ne mafi kololuwar mutumin da ya kamata yayi adalci a ban kasa ko da kuwa akan waye, sai dai da dama sun gagara yin haka akan Jonathan.
A yanzu a wannan karon, da aka samu sauyin Gwamnati Boko Haram suka kaddamar da kai sabbin hare hare, Gwamnan Borno Kashimu shatima yake kiran ai musu ahuwa duk kuwa da irin mummunan ta'adi da barnar da suka tafka. Ammam dai duk da haka, lokaci na kara tafiya gaskiyar wannan lamari zata cigaba da bayyana.
Ba mamaki, daga masu wancan ikirari na baya suce ai Boko Horam ta kare yanzu kuma ISIS ne suke kaddamar da sabbin hare hare dan tabbatar da zargin da sukaiwa Jonathan a baya. Allah ka bamu lafiya da zaman lafiya, Allah ka bayyanawa al'umma gaskiya akan wannan ta'addanci, Ya Allah duk mai hannu a ciki ka tona masa asiri kowa ya ganshi.
03-06-2015