Sunday, March 13, 2016

Ta'addancin Da Shiah Sukaiwa Mai Martaba Sarkin Hadejia


TA'ADDANCIN 'YAN SHIAH GA MAI MARTABA SARKIN HADEJIA

A ranar Juma'ar wannan makon mai karewa ne, 'yan Shiah suka yiwa fadar Mai Martaba Sarkin Hadejia tsinke, inda suka aikata Ta'addqnci ga Mai Martaba Sarki. Rahotanni sun nuna cewsr 'yan Shiah sun shiga harabar Fadar sarki da nufin zanga zanga dauke da kwalaye da takardun bango da suke nuni da a saki Shugabansu da ke tsare hannun sojoji.

Wannan dalili yasa 'Yan Shiah sukaiwa Mai Martaba sarki ihu da jifan ayarin Dogaransa da duwarwatdu da kwalaye. Wannan kadan ne daga cikin irin ayyukan Ta'addanci da Shiah suka jima suna aikatawa a Duniya. Su din daman wasu mutane ne da basa kaunar zaman lafiya a ko da yaushe.

Dan haka muna kira ga mahukunta da su dauki mataki na hana yin duk wata zanga zangar 'Yan Shiah a ko ina a kuma ko da yaushe. Ba daidai bane, hukumomi su zubawa wasu mutane ido suna daukar doka a hannunsu suna yiwa mutane abinda suka ga dama ba tare da an taka musu birki ba.

Muna kara yin Adduah ta musamman ga Mai Martaba Sarkin Hadejia, Allah ya kara masa lafiya. Ya kare shi daga dukkan sharrin masu sharri. Ya yi masa garkuwa da garkuwarsa. Allah ya daukaka darajarsa da masarautarsa. Allah ya karawa Sarki Lafiya. Wadannan Shedanun mutane Allah kai mana maganinsu a duk inda suke.

Yasir Ramadan Gwale
13-03-2016

Wednesday, March 9, 2016

Yiwa Yunusa Yellow Shari'ah Shi Ne Adalci


YI WA YUNUSA YELLOW SHARI'A SHI NE ADALCI 

Sau da dama rashin sani da ad'ifar k'abilanci kan hana mutane ganin gaskiya. Mutane da yawa basu fahimci hakikanin abinda ake tuhumar Yunusa Yellow akai ba, dangane da batun Ese Oruru (A'isha). Kawai abinda mafiya yawa suke kallo shi ne batun addini, da kuma shi wanda abin ya faru da shi, wato Musulmi, kuma Bahaushe 'dan Kano ko Arewa. Yawancin mutane a tunaninsu idan Bahaushe Musulmi ya aikata wani laifi, komai muninsa, tilas kafatanin Musulmi su goyi bayansa, musamman ma ace abin ya had'a da wanda ba Musulmi ba. Amma abinda muke kira a koda yaushe shi ne: ayi Adalci, don Musulunci shi ke kira ga yin adalci fiye da komai.

Tunanin wasunmu da yawa, gani suke idan mutanan kudu ko wad'anda ba Musulmi ba sun yi mana rashin adalci, tilas ne mu ma idan mun samu dama mu yi musu rashin adalci. Sun manta cewar addinin Musulunci da muke 'kafafa ko tutiya  da shi ya horemu da yin adalci. Saboda Adalci Allah ya azabtar da Bil Adama a dalilin ya cutar da dabba. Annabi (SAW) ya gaya mana cewar, Allah ya azabtar da wata mata a dalilin kyanwa, sabida ta cutar da dabbar!

Wannan batun na Ese Oruru (Aisha) yayi matukar daukan hankalin mutane fiye da batun Abdul Nyass lokacin da yayi kalaman ridda, har wasu tsiraru suna maganganu na rashin kyautawa, a tunaninsu hakan zai nuna cewar su masu kishin Musulunci ne ko kishin Arewa. Wannan ba daidai bane, mutum ya tafka kuskure kawai saboda namu ne Musulmi d'an Arewa mu goyi bayan abinda ya aikata ba tare da tuntubar me addini yace ba kafin ya aikata. 

Ga dukkan alamu wannan matashi bai nemi sanin meye addinin Musulunci yace ba akan abinda ya aikata, kafin ya aikata din,  wanda a hakan kuma wasu ke ganin tilas kowane Musulmi ya goyi bayansa, haka kuma, bai nemi sanin tanadin dokar kasar nan mai al'ummar da ke da ma'abuta addinai daban daban ba. Abu na farko dai, a tuhumar da ake yiwa wannan matashi, babu batun addini. A cikin jerin tuhumar da akai masa babu inda aka ambaci ana tuhumar sa da cewar ya Musuluntar da wannan yarinya da yardarta ko babu. Batu na addini kam, yarinya ta Musulunta, muna fatan Allah Ya tabbatar da duga-duganta akan turba ta Musulunci, Ya kare ta da dukkan kariyar Sa, Yayi mata garkuwa da dukkan garkuwar Sa. 

Bayan haka, wannan matashi, ya tabbatar da cewar shi ya kawo ta Kano daga Bayelsa, kuma ya amince cewar yana tarawa da ita tun a garin su Bayelsa, wannan yasa yarinya ta samu juna biyu mai kimanin watanni biyar. To anan, kawai sai mu goyi bayan barna? Yaro ya dauko yarinya daga garinsu bayan yayi mata ciki, sannan kuma yanzu sai a zo da batun addini a fake don a nemar masa kariya?

Abin mamaki ne, ka ji mutane masu hankali da ilimi suna fadin kalamai marassa kan gado, kamar cewa: wai Mu Musulmi mun ji kunya! Kuma mutanan da aka fi zargin sune Malamai da Sarakuna da Shugabanni wai suna gani anzo an tafi da dan uwanmu za a je wulakanta Musulmi da sauran ire-iren wadannan kalamai masu cike da wauta da rashin sani da tunzura al'umma. 

Hakika wadancan kalaman shiririta ne da zafin kai na babu gaira babu dalili. Batun da yake gaban Shari'ah me kuma mutum yake fatan a yi? Ko kuwa, muna so Malamai da Sarakuna su hana a yi masa Shari'ah saboda shi Bahaushe ne dan Kano Musulmi? Dole dai dayan biyu za a yi, ko dai a same shi da laifi ai masa hukunci daidai da abinda ya aikata bisa tanadin dokar kasa, ko kuma a ce ba shi da laifi. Dole dayan biyu ya faru. To me kuma, muke son ayi?

Wasu ma saboda tsabar rudani da rashin sanin makama, cewa suke wai akwai wani Pastor daga kudu da yazo Arewa ya saci 'yayan Musulmi ya kai su kudu zai maida su kiristoci. Abubuwan tambaya ga masu wannan shirbici, sune : 
Shin sai yanzu ne kuka samu labarin satar  yaran? 
Idan ka kwana biyu da masaniya akai, shin a bayan wani mataki ka dauka? 
Me ya hana ku kai shi Pastor din zuwa kotu indai batun gaskiya ne?
Kuma ma, shin yaran nan da muka bari a tituna suna watangarirya suna gararambar neman abinda zasu ci, cikin tsummokarai da datti da kazanta da rashin nagartacciyar koyarwar addini, wai sune muke nuna kishin riya akan su? A tsakanin mu ne fa mu Mutanan Arewa Musulmi ake maganar akwai Almajirai sama da Miliyan goma sha biyu (12,000,000), me mu kayi na taimaka musu fita daga halin kunci da suke ciki? 

Bamu iya mu taimakawa wanda ke cikin halin bukata ba, sai wanda ya aikata laifin da ya hada da dan kudu, wanda ba Musulmi ba, sannan ne kishi da son al'ummar mu zai motsa? Ya kamata mu daina yaudarar  kawukan mu, mu gayawa juna  gaskiya. Wannan matashi, Yunusa Yellow dan uwanmu ne, yayi kuskure ya aikata ba daidai ba, ya kamata a nuna masa kuskurensa, don hakan ya zama izna ga na baya.

Haka kuma, yana da kyau mutane su fahimta, a cikin Shari'ah da kuma jerin tuhumar da aka yi wa wannan matashi, babu inda aka zarge shi da cewar ya tursasawa yarinya bin addinin Musulunci. Balle wasu su rud'a mutane da cewar, ai don ya Musuluntar da ita ne akai masa haka. Wannan Sam ba gaskiya bane, ai a kasar Bayelsa akwai Musulmi 'yan asalin yankin kuma suna rayuwa cikin 'yanci kamar kowane d'a, ballantana kuma batun Musuluntar wannan yarinya, batu ne da kungiyar kare hakkokin Musulmi kamar MURIC tana sane da shi (wanda tunin ma ta fidda matsayan ta akan matashin yayi ba daidai ba) da masu ayyukan da'awa da kula da sabbin Musulunta suna sane. Allah ka nuna mana gaskiya ka bamu ikon binta, ka nuna mana karya ka bamu ikon kauce mata.

Yasir Ramadan Gwale 
09-03-2016

Thursday, March 3, 2016

Mayar Da Ese Oruru Gaban Iyayanta Shi Ne Abinda Ya Dace


MAYAR DA ESE ORURU GABAN IYAYANTA SHI NE ABINDA YA DACE

Ni kam banga wani abin tashin hankali dan an mayar da wannan yarinyar gaban iyayanta ba. Iyayan ta mahaifa suna da hakki akanta, dan haka ba wani abin tayar da jijiyar wuya bane dan an mika musu ita. Rayuwar Musulmi cike take da abin koyi, ga duk wanda ya fahimci darussan da ke cikin SULHUL HUDAIBIYYA da mayar da sahabi Abu Jandal Ibn Suhailu Ibn Amri r.a da Annabi Sallallahu Alaihi Wa Sallam yayi ga iyayen sa mushrikai a tsakiyar sulhun, na meye nasa zai tayar da hankali dan an ce yarinya ta koma ga iyayanta? 

Addinin Musulunci na Allah ne, kuma da kaddarawarsa ne Subhanahu Wata'ala, komai yake tabbata. Wannan yarinya da ta Musulunta, indai ta Musulunta don Allah da neman yardarsa, Allah zai bata kariya a duk inda take. Haka kuma, a Musulunci komai yana da ka'ida da kuma sharadi. Babu yadda za a ce mutum ya dauko 'yar mutane ya aureta ba tare da sanin iyayanta ko da amincewar shuwagabanni ba kuma ace auren ingantacce ne. 

Ni ina ganin indai ba tsananin zafin kai da kafiya ba, ai wannan lamari mai sauki ne. Tunda yarinya ta koma gaban iyayanta, sai shi yaron yabi hanya sahihiya dan neman aurenta a wajen waliyyanta. Ba yau aka fara yin aure tsakanin mutanan kudu da Arewa ba, ba kuma yau ne Musulmi suka fara auren wanda ba Musulmi ba su musuluntar da su. Jiya naji Malam Aminu Daurawa yayi bayani gamsasshe akan wannan batun. Allah ya bamu lafiya da zaman lafiya. Ya Allah ka cigaba da baiwa addininka kariya.

Yasir Ramadan Gwale 
03-03-2016

Tuesday, March 1, 2016

Ana Fakewa Da Guzuma . . .


ANA FAKEWA DA GUZUMA . . .
Bayan da asirin su Malam Ibrahim Zakzaky ya tonu, kuma Allah ya kama su ta hanyar turo musu da Sayyid Ayatollah Buratai Yusuf ya darkake su darkakewa. Muna fatan abinda ya samesu na wannan jarabawa ya sa masu hankali da fahimta daga cikinsu su fahimci gaskiya su karbeta, su gane turba ta gaskiya su kama Sunnar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam su daina Shiah domin b'ata ce mabayyaniya. Muna fatan abinda ya same su ya zama ukuba anan duniya ga duk masu zagi da aibata Iyalai da abokan Ma'aiki Sallallahu Alaihi Wasallam.
Da yake macizai ne basa gina rami da kansu, sukan fake da guzuma su sari karsana. Su dai sun san karyarsu ta sha karya ba zasu iya fitowa fili su zagi ko Aibata Sayyadi Ayatollah Burtai Yusuf ba, a dan haka sai suka fake da siyasa suna zagin Shugaban kasa sabida da d'an siyasa ne.
Shugaba ko wane iri ne yana da kima da daraja a Musulunci, haka kuma zaginsa fasikanci ne. To amma su dama suje nema dan su yiwa shugaban kasa tatas, su amayar da miyagun maganganun akansa. Dan haka daga zarar wani yayi maganganu na suka ko hamayya da Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari sai su fake da wannan suyi ta zagi da cin mutunci. Alhali kuma su din turbar siyasa Dagutanci ne a wajensu balle muce su shigo fagen siyasa a buga da su.
Hamayya ko kalubalanta a siyasar Demokaradiyyar da Shiah suka kafirta Halal ne. Mun gamsu, mun kuma Amincewa da haka, cewar a kalubalanci Gwamnati kuma ai mata hamayya. Amma su 'yan Shiah abinda suke yi ba haka bane. Suna amfani da damar 'yan hamayya suna cin zarafi da mutuncin Shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Allah ka nuna mana gaskiya mu fahimceta kuma ka bamu ikon binta. Ka nuna mana karya kamar yadda ka nuna Mana Shaianci mu gane karya ne ka bamu ikon kauce mata, kamar yadda muka kaucewa Shiah kuma muke neman tsari da ita. Allah ka taimaki kasarmu ka bamu lafiya da zaman lafiya.
Ya Allah kasa wannan abun da Sayyid Ayatollah Buratai Yusuf yayi shi ne silar kawo karshen duk wani makirci da makida ta 'Yan Shiah gurbatattu lalatattu. Allah ka kare kasarmu daga maguanci da kafircin Shiah.
01-03-2016